Home General PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

Jam’iyyar PDP ta yi watsi da sakamakon zaben jihar Ondo, bayan hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC ta ayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Gwamna Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben.

PDP ta ce za ta garzaya kotu domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar.

Muƙaddashin hulda da manema labarai na Jam’iyyar PDP ya yi zargin cewa an tafka magudi da amfani da karfin tsiya aka kada dan takararsu Mr. Agboola Ajayi.

Hakan na zuwa ne bayan wasu korafe-korafe da wakilin jam’iyyar PDP na karamar hukumar Idanre ya yi zargin cewa ba a yi zabe a unguwar Ofosun Oniseri ba, yayin da aka kori ƴan PDP, aka ƙwace ƙuri’u a Alade.

Alhaji Abdullahi Ibrahim ya yi zargin cewa zaben ya saɓa wa tsarin dimokuradiyya inda ya ce za su dauki mataki na gaba.

“Za mu garzaya kotu a matsayinmu na jam’iya, da muke sukar lamirin wannan zaɓe, mun yi tir da Allah wadai da hukuncin da hukumar zaɓe ta bayar.”

Tuni jam’iyyar PDP ta ce za ta yi nazari kan zaben da kuma sakamakonsa kafin ɗaukar mataki na gaba kan abin da ta kira kare dimokuraɗiyya a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp