Home Bincike Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya sakamakon rikici –...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya sakamakon rikici – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda yunwa ke kara kamari a arewa maso gabas na Najeriya, musamman a jihohin Borno, Adamawa da Yobe, inda fiye da mutane miliyan 3.7 ke fuskantar matsananciyar rashin abinci.

A cewar rahoton, rikicin da ya dauki shekaru 16 ya durƙusar da kasuwanci da hanyoyin samun aiki, wanda hakan ya tilastawa mutane dogaro da ƙananan gonaki don rayuwa.

A Dikwa, manoma na tashi da safe su ratsa tafiya mai tsawo domin yin noma na ‘yan awanni kafin su koma gida.

Churi Ibrahim, wani tsohon manomi dan shekara 70 da ke ciyar da iyalinsa goma, ya ce farashin abinci ya yi tashin gwauron zabi, kuma kudin ɗinki da yake samu da dare bai isansu.

Modu Umar, wani shugaban al’umma, ya bayyana cewa yunwa tana haddasa cututtuka kamar gudawa a cikin yara da manya saboda rashin abinci da magani.

“Mutane na fita nesa su tara itace domin samun kudin siyan abinci.” in ji shi.

ICRC dai ta ce ta fara wani shiri na taimakawa noma ta hanyar raba iri da kayan aikin noma ga sama da iyalai 21,000 a bana, domin tallafa musu a lokutan kaka da rani.

“Ana kuma shirin rarraba famfunan ban-ruwa masu aiki da hasken rana domin noman rani.” in ji ƙungiyar ICRC.

Shugabar ofishin ICRC a Maiduguri, Diana Japaridze, ta ce ana fargabar lokacin Ƙarancin abinci daga Yuli zuwa Satumba, inda mutane ke buƘatar sayen abinci, amma Ƙarancin kudi yana hana su cika buƙata.

Wata uwa mai yara biyar, Bintu Konto, ta ce: “Wasu lokuta muna kwana da yunwa har kwana biyu zuwa uku. Idan Allah ya kawo wani abu, sai mu ci.”

Ƙungiyar ICRC na aiki a Borno tun 2012 inda take taimakawa al’ummomin da rikici ya shafa da kuma kare martabar fararen hula bisa dokokin Geneva na 1949.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp