Fadar shugaban ƙasa ta yi watsi da rahoton Bankin Duniya kan Talauci

Fadar shugaban ƙasa ta maida martani kan rahoton Bankin Duniya da ya ce mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci a Najeriya, inda ta ce ƙididdigar ba ta nuna hakikanin halin da ake ciki a ƙasar ba.

A cewar fadar shugaban ƙasa, Bankin Duniya ya yi amfani da ƙa’idar duniya wadda ke ɗaukar duk wanda ba ya samun sama da dala $2.15 a rana a matsayin talaka.

Wannan ƙa’ida an kafa ta ne tun shekarar 2017, kuma idan aka fassara ta zuwa kuɗin Najeriya a yau, ta kai kusan Naira 100,000 a wata fiye da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 kenan.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Fadar shugaban ƙasa ta fitar wanda Sunday Dare, mai magana da yawun shugaban ƙasa ya fitar a shafinsa na X.

‘Bayanan da Bankin Duniya ya dogara da su tsofaffi ne tun daga shekarar 2018/2019, kuma ba su haɗa da tattalin arzikin yanzu ba. Saboda haka, gwamnati ta bayyana cewa wannan adadi misali ne na ƙididdigar duniya, ba ainihin yanayin da ake ciki a shekarar 2025 ba.”

A cewar fadar shugaban ƙasa, abin da ya fi muhimmanci shi ne hanyar da ake bi wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa, amma kuma Bankin Duniya ta ce sauye-sauyen Tinubu ba su rage talauci ba.

Ta ce “gwamnatin Shugaba Tinubu tana mai da hankali ne wajen rage wahalar tattalin arziki ta hanyar shirye-shirye na musamman kamar tallafin kuɗi ga talakawa, da bashin karatu na ɗalibai, da sauransu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com