Home Labarai Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya

Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya

Haɗakar kwamitin majalisar dattawa da ta wakilan tarayya mai duba batun gyaran kundin tsarin mulki ta amince da ƙirƙirar sabbin jihohi guda shida a Najeriya.

Wannan mataki ya biyo bayan taron ƙara wa juna sani na kwanaki biyu da kwamitin ya gudanar a jihar Legas, ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, tare da takwaransa na majalisar wakilai, Benjamin Kalu.

A taron, an tattauna kan buƙatu 69 da suka haɗa da neman kafa sabbin jihohi 55 da ƙananan hukumomi 278, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Daga cikin waɗannan buƙatun, kwamitin ya zaɓi amincewa da ƙirƙirar jihohi guda shida — ɗaya daga kowace shiyyar ƙasar — domin tabbatar da daidaito a rabon jihohi.

Idan wannan shawarwarin ya samu amincewar doka, adadin jihohin Najeriya zai karu daga 36 zuwa 42.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp