Home Labarai Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya

Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya

Haɗakar kwamitin majalisar dattawa da ta wakilan tarayya mai duba batun gyaran kundin tsarin mulki ta amince da ƙirƙirar sabbin jihohi guda shida a Najeriya.

Wannan mataki ya biyo bayan taron ƙara wa juna sani na kwanaki biyu da kwamitin ya gudanar a jihar Legas, ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, tare da takwaransa na majalisar wakilai, Benjamin Kalu.

A taron, an tattauna kan buƙatu 69 da suka haɗa da neman kafa sabbin jihohi 55 da ƙananan hukumomi 278, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Daga cikin waɗannan buƙatun, kwamitin ya zaɓi amincewa da ƙirƙirar jihohi guda shida — ɗaya daga kowace shiyyar ƙasar — domin tabbatar da daidaito a rabon jihohi.

Idan wannan shawarwarin ya samu amincewar doka, adadin jihohin Najeriya zai karu daga 36 zuwa 42.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp