Home Labarai Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya

Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya

Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU) ta musanta wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke zarginta da hannu a cikin aikin ƙirƙirar makaman nukiliya a Najeriya.

Daraktan yada labarai na jami’ar, Auwalu Umar, ya bayyana a wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar cewa bidiyon da aka ƙirƙira ta hanyar AI ba gaskiya ba ne, kuma manufarsa ita ce yaudarar jama’a game da shirin makamashin nukiliya a Najeriya.

Ya ce zargin cewa masana na ABU sun taɓa samun kayan aikin ƙirƙirar makami daga cibiyar AQ Khan ta Pakistan ko yin gwajin uranium a Kaduna a shekarun 1980 ba gaskiya bane .

Umar ya ƙara da cewa a lokacin da ake zargin, yawancin masana a cibiyar binciken makamashin nukiliya ta jami’ar (CERT) suna ci gaba da karatu a ƙasashen waje, kuma babu wata shaida da ke nuna an taɓa yin aikin da ya saba wa doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp