Home Labarai Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya

Jami’ar ABU ta musanta labarin samar da makamin Nukiliya

Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU) ta musanta wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke zarginta da hannu a cikin aikin ƙirƙirar makaman nukiliya a Najeriya.

Daraktan yada labarai na jami’ar, Auwalu Umar, ya bayyana a wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar cewa bidiyon da aka ƙirƙira ta hanyar AI ba gaskiya ba ne, kuma manufarsa ita ce yaudarar jama’a game da shirin makamashin nukiliya a Najeriya.

Ya ce zargin cewa masana na ABU sun taɓa samun kayan aikin ƙirƙirar makami daga cibiyar AQ Khan ta Pakistan ko yin gwajin uranium a Kaduna a shekarun 1980 ba gaskiya bane .

Umar ya ƙara da cewa a lokacin da ake zargin, yawancin masana a cibiyar binciken makamashin nukiliya ta jami’ar (CERT) suna ci gaba da karatu a ƙasashen waje, kuma babu wata shaida da ke nuna an taɓa yin aikin da ya saba wa doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp