Home Labarai Mayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a...

Mayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a Borno

Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta ɗauki matakin gaggawa wajen nazari tare da gyara harkokin tsaron sararin samaniyar ƙasar domin daƙile amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare a ƙasar.

Zulum ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a garin Mafa bayan wani hari da ƴan Boko Haram suka kai kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

“Babban abin da nake so in yi magana a nan shi ne amfani da jirage marasa matuƙa. An faɗa min cewa sun yi amfani da jirage marasa matuƙa a Dikwa. Wannan abin tashin hankali ne matuƙa.”

“Yawaitar jirage marasa matuƙa a hannun maƙiya abu ne mai matuƙar haɗari. Dole mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen daƙile wannan sabon salon,” in ji Zulum.

Gwamnan ya ce akwai buƙatar a ƙara tsaurara matakan kariya a bakin iyakokin ƙasar, “sannan akwai buƙatar a ƙara inganta tsaron sararin samaniyarmu. Wannan mataki ne da ya kamata a ɗauka cikin gaggawa ba tare da ɓata lokaci ba.”

Zulum ya yi kira ga al’ummar jihar da su riƙa ba jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar kai su bayana sirri da za su taimaka musu wajen magance matsalolin tsaro.

“Maganar gaskiya mun samu labarin za a kai hari a Mafa, kuma dukkan hukumomin da suka cancanci sani an faɗa musu. Wannan ne ya sa nake tunanin akwai zagon-ƙasa a harkar. Shi ya sa nake a zo a duba tare da yin gyara.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp