Home Labarai Mayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a...

Mayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a Borno

Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta ɗauki matakin gaggawa wajen nazari tare da gyara harkokin tsaron sararin samaniyar ƙasar domin daƙile amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare a ƙasar.

Zulum ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a garin Mafa bayan wani hari da ƴan Boko Haram suka kai kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

“Babban abin da nake so in yi magana a nan shi ne amfani da jirage marasa matuƙa. An faɗa min cewa sun yi amfani da jirage marasa matuƙa a Dikwa. Wannan abin tashin hankali ne matuƙa.”

“Yawaitar jirage marasa matuƙa a hannun maƙiya abu ne mai matuƙar haɗari. Dole mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen daƙile wannan sabon salon,” in ji Zulum.

Gwamnan ya ce akwai buƙatar a ƙara tsaurara matakan kariya a bakin iyakokin ƙasar, “sannan akwai buƙatar a ƙara inganta tsaron sararin samaniyarmu. Wannan mataki ne da ya kamata a ɗauka cikin gaggawa ba tare da ɓata lokaci ba.”

Zulum ya yi kira ga al’ummar jihar da su riƙa ba jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar kai su bayana sirri da za su taimaka musu wajen magance matsalolin tsaro.

“Maganar gaskiya mun samu labarin za a kai hari a Mafa, kuma dukkan hukumomin da suka cancanci sani an faɗa musu. Wannan ne ya sa nake tunanin akwai zagon-ƙasa a harkar. Shi ya sa nake a zo a duba tare da yin gyara.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp