Home Labarai Mayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a...

Mayakan Boko Haram sun fara kai hari da jirage marasa matuki a Borno

Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta ɗauki matakin gaggawa wajen nazari tare da gyara harkokin tsaron sararin samaniyar ƙasar domin daƙile amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare a ƙasar.

Zulum ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a garin Mafa bayan wani hari da ƴan Boko Haram suka kai kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

“Babban abin da nake so in yi magana a nan shi ne amfani da jirage marasa matuƙa. An faɗa min cewa sun yi amfani da jirage marasa matuƙa a Dikwa. Wannan abin tashin hankali ne matuƙa.”

“Yawaitar jirage marasa matuƙa a hannun maƙiya abu ne mai matuƙar haɗari. Dole mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen daƙile wannan sabon salon,” in ji Zulum.

Gwamnan ya ce akwai buƙatar a ƙara tsaurara matakan kariya a bakin iyakokin ƙasar, “sannan akwai buƙatar a ƙara inganta tsaron sararin samaniyarmu. Wannan mataki ne da ya kamata a ɗauka cikin gaggawa ba tare da ɓata lokaci ba.”

Zulum ya yi kira ga al’ummar jihar da su riƙa ba jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar kai su bayana sirri da za su taimaka musu wajen magance matsalolin tsaro.

“Maganar gaskiya mun samu labarin za a kai hari a Mafa, kuma dukkan hukumomin da suka cancanci sani an faɗa musu. Wannan ne ya sa nake tunanin akwai zagon-ƙasa a harkar. Shi ya sa nake a zo a duba tare da yin gyara.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp