Home Labarai Babu wasu bayanan an yi wa masu bin wani addini kisan ƙare...

Babu wasu bayanan an yi wa masu bin wani addini kisan ƙare dangi – Sultan

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya bayyana cewa babu wasu bayanan da ke nuna cewa an yi wa masu bin wani addini ko Kirista ko Musulmi kisan ƙare dangi a Najeriya.

Sarkin ya faɗi hakan ne a yayin buɗe taron Majalisar Sarakunan Arewa a Birnin Kebbi, 2025.

Sarkin ya ce, “Babu yadda za a kashe wani mutum, ko Musulmi ko Kirista, ba tare da sanin sarakuna ko shugabannin al’ummar da wannan mutumin ya fito ba.”

Ya kuma ƙalubalanci kowa, a cikin gida ko waje, da su kawo hujja ta gaske kan wani kisan ƙare dangi a Najeriya.”

Sultan Sa’ad ya gargadi jama’a da kada su gaskata duk abin da suka gani ko karanta a kafafen sada zumunta, yana mai cewa yawancin bayanan da ake yaɗawa ba gaskiya bane.

“Yawancin abin da aka wallafa a kafafen sada zumunta ba gaskiya bane. Dole mutane su tabbatar da sahihancin bayani kafin su ɗauke shi a matsayin gaskiya,” in ji shi.

Sarkin ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta hanzarta tsara dokoki da za su kula da ayyukan masu amfani da kafafen sada zumunta domin rage yaɗa labaran ƙarya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp