Home Labarai Za ayi bincike kan masu laifin da Tinubu ya yiwa Afuwa

Za ayi bincike kan masu laifin da Tinubu ya yiwa Afuwa

Babban ministan shari’a na Najeriya kuma babban lauyan gwamnati, Lateef Fagbemi, ya bayar da umarni ga hukumomi da dama su gudanar da bincike kan jerin sunayen masu laifin da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yi wa afuwa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Fagbemi ya bayyana hakan ne a yayin taron Majalisar mahukunta da aka gudanar a ranar Alhamis, 9 ga Oktoba, 2025. in da ya ce hukumomin da za su gudanar da wannan binciken sun haɗa da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa (EFCC), hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA), da kuma Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya.

Ana hasashen cewa binciken zai iya kai ga cire fiye da rabin sunayen mutanen da aka yi wa afuwa.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu dai na jira a mika masa jerin sunayen da aka tantance domin ya sanya hannu na karshe, a yunkurin tabbatar da cewa duk wanda zai amfana daga afuwar ya cancanta.

Tinubu dai ya yi amfani da ikon da ƙundin tsarin mulki ya ba shi wajen yi wa mutum 175 da aka samu da laifuka daban-daban afuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp