Home Labarai Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika sakon taya murna ga tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, yayin da yake bikin cikar shekarar 69 da haihuwar a ranar 21 ga Oktoba, 2025.

A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Litinin, Shugaba Tinubu ya yaba da gudunmawar da Sanata Kwankwaso ya bayar wajen ci gaban ƙasa ta fannoni daban-daban, ciki har da kasancewarsa Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai a zamanin jamhuriya ta uku da Ministan Tsaro da Gwamnan Jihar Kano sau biyu, da kuma Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya.

Shugaban ƙasa ya bayyana cewa, tasirin siyasar Kwankwaso a Arewacin ƙasar, musamman a Kano, na nuni da irin siyasar jin ƙai da kishin jama’a da ya gada daga marigayi Malam Aminu Kano da marigayi Alhaji Abubakar Rimi.

“Sanata Kwankwaso aboki ne kuma abokin aiki wanda muka yi aiki tare a majalisar dokoki ta tarayya a shekarar 1992, sannan muka zama gwamnoni a shekarar 1999. Mun kuma yi aiki tare wajen kafa jam’iyyar APC. Ko da yake daga baya ya bar jam’iyyar don kafa NNPP, abin lura ne cewa har yanzu yana cikin tafiyar ci gaba,” in ji Shugaba Tinubu.

A daidai lokacin da ake ta jita-jita game da yiwuwar sabuwar dangantaka ko sauya sheka tsakanin manyan ‘yan siyasa, masu lura da al’amura sun bayyana sakon na Tinubu a matsayin alamar gina gada da kuma ƙarfafa zumunta a siyasa.

Shugaban ƙasa ya yi wa Sanata Kwankwaso fatan alheri, lafiya, da ƙarin shekaru masu amfani ga ƙasa da al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp