Home Labarai Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Tinubu ya taya Kwankwaso munar cika shekaru 69 a duniya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika sakon taya murna ga tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, yayin da yake bikin cikar shekarar 69 da haihuwar a ranar 21 ga Oktoba, 2025.

A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Litinin, Shugaba Tinubu ya yaba da gudunmawar da Sanata Kwankwaso ya bayar wajen ci gaban ƙasa ta fannoni daban-daban, ciki har da kasancewarsa Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai a zamanin jamhuriya ta uku da Ministan Tsaro da Gwamnan Jihar Kano sau biyu, da kuma Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya.

Shugaban ƙasa ya bayyana cewa, tasirin siyasar Kwankwaso a Arewacin ƙasar, musamman a Kano, na nuni da irin siyasar jin ƙai da kishin jama’a da ya gada daga marigayi Malam Aminu Kano da marigayi Alhaji Abubakar Rimi.

“Sanata Kwankwaso aboki ne kuma abokin aiki wanda muka yi aiki tare a majalisar dokoki ta tarayya a shekarar 1992, sannan muka zama gwamnoni a shekarar 1999. Mun kuma yi aiki tare wajen kafa jam’iyyar APC. Ko da yake daga baya ya bar jam’iyyar don kafa NNPP, abin lura ne cewa har yanzu yana cikin tafiyar ci gaba,” in ji Shugaba Tinubu.

A daidai lokacin da ake ta jita-jita game da yiwuwar sabuwar dangantaka ko sauya sheka tsakanin manyan ‘yan siyasa, masu lura da al’amura sun bayyana sakon na Tinubu a matsayin alamar gina gada da kuma ƙarfafa zumunta a siyasa.

Shugaban ƙasa ya yi wa Sanata Kwankwaso fatan alheri, lafiya, da ƙarin shekaru masu amfani ga ƙasa da al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp