Home General Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Farfesa Joash Amupitan, a matsayin shugaban hukumar zaɓe ta ƙasar INEC.

Majalisar ƙarƙashin jagorancin shugabanta Godswill Akpabio ta tabbatar da Amupitan ne bayan kammala tantance shi, inda ya amsa tambayoyin da ƴan majalisar suka yi masa.

Nan gaba kaɗan ne ake sa ran shugaba Bola Tinubu zai rantsar da shi domin kama aiki gadan-gadan.

A ranar 7 ga watan da muke ciki na Oktoba ne tsohon shugaban hukumar, Farfesa Mahmoud Yakubu ya kammala wa’adin mulkinsa na biyu a matsayin shugaban hukumar ta INEC, bayan shafe shekaru 10.

Tun a watan Oktoban 2015 ne marigayi tsohon shugaban Najeriya, Muhamamdu Buhari ya naɗa Farfesa Mahmoud Yakubu, a matsayin shugaban hukumar INEC, kana ya sabunta naɗin nasa a shekarar 2020.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp