Home General Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Farfesa Joash Amupitan, a matsayin shugaban hukumar zaɓe ta ƙasar INEC.

Majalisar ƙarƙashin jagorancin shugabanta Godswill Akpabio ta tabbatar da Amupitan ne bayan kammala tantance shi, inda ya amsa tambayoyin da ƴan majalisar suka yi masa.

Nan gaba kaɗan ne ake sa ran shugaba Bola Tinubu zai rantsar da shi domin kama aiki gadan-gadan.

A ranar 7 ga watan da muke ciki na Oktoba ne tsohon shugaban hukumar, Farfesa Mahmoud Yakubu ya kammala wa’adin mulkinsa na biyu a matsayin shugaban hukumar ta INEC, bayan shafe shekaru 10.

Tun a watan Oktoban 2015 ne marigayi tsohon shugaban Najeriya, Muhamamdu Buhari ya naɗa Farfesa Mahmoud Yakubu, a matsayin shugaban hukumar INEC, kana ya sabunta naɗin nasa a shekarar 2020.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp