Home Labarai Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya

Za’a samar da sabbin jihohi 6 a Nijeriya

Haɗakar kwamitin majalisar dattawa da ta wakilan tarayya mai duba batun gyaran kundin tsarin mulki ta amince da ƙirƙirar sabbin jihohi guda shida a Najeriya.

Wannan mataki ya biyo bayan taron ƙara wa juna sani na kwanaki biyu da kwamitin ya gudanar a jihar Legas, ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, tare da takwaransa na majalisar wakilai, Benjamin Kalu.

A taron, an tattauna kan buƙatu 69 da suka haɗa da neman kafa sabbin jihohi 55 da ƙananan hukumomi 278, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Daga cikin waɗannan buƙatun, kwamitin ya zaɓi amincewa da ƙirƙirar jihohi guda shida — ɗaya daga kowace shiyyar ƙasar — domin tabbatar da daidaito a rabon jihohi.

Idan wannan shawarwarin ya samu amincewar doka, adadin jihohin Najeriya zai karu daga 36 zuwa 42.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp