Home Labarai Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a...

Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da kafa Runduna ta Musamman (Special Task Force) domin magance barazanar tsaro a tashoshin mota da sauran muhimman wuraren taruwar jama’a a fadin jihar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi. Sanarwar ta ce matakin na nuna kudurin gwamnati na hana kutsen masu aikata laifi, musamman a wuraren shiga da fita na birnin Kano.

An bayyana tashoshin mota a matsayin wuraren da ke da hadarin tsaro, sakamakon yawaitar zirga-zirga da kuma kamun wasu da ake zargi da aikata laifi a tashar mota ta Kofar Ruwa kwanan nan.

Rundunar za ta gudanar da sa ido, tattara bayanan sirri da hadin gwiwar ayyukan tsaro a tashoshin mota, gidajen mai da sauran wuraren jama’a, domin dakile barazana tun kafin ta tsananta. Gwamnan ya jaddada manufar gwamnatinsa ta ba da cikakken goyon baya ga hukumomin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp