Home Labarai Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci majalisar dattawar ƙasar ta amince da naɗin Engr Saidu Aliyu Mohammed, a matsayin sabon shugabannin Hukumar Kula da Albakatun mai na kan tudu NMDPRA, bayan murabus daga matsayin da Engr Farouk Ahmed ya yi.

A cikin wata sanarwa da mai taimakawa shugaba Tinubu wajen hulda da kafafen yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ta ce shugaban ya kuma nemi majalisar ta amince ya naɗa Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan, a matsayin magajin Gbenga Komolafe, da ke shugabantar hukumar kula da albarkatun mai na cikin ruwa.

Tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari ne ya naɗa su a shekarar 2021, domin jagorantar hukumomin biyu da dokar masana’antar mai ta ƙasar ta ƙirƙiro.

Wannan dai na zuwa ne bayan da a ranar lahadin da ta gabata, shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote, Aliko Dangote ya zargin Engr Farouk Ahmed da biya wa ƴaƴansa 4 kuɗin makaranta a Switzerland, da suka kai dala miliya biyar.

Tuni dai hukumar yaƙi da almundahana ta ICPC a Najeriya, ta tabbatar da karɓar ƙorafin da Ɗangote ya shigar gabatanta, kuma ta ce za ta yi bincike akai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp