Home Labarai Gwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen waje

Gwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen waje

Gwamnatin Najeriya ta haramta fitar da itace da kayayyakin da suka shafi itace zuwa ƙasashen waje a faɗin ƙasar baki ɗaya, tare da soke dukkan lasisi da izini da aka bayar a baya kan irin wannan kasuwanci.

Sanarwar ta fito ne a ranar Laraba daga bakin ministan muhalli, Balarabe Lawal, yayin taron malalisar ƙasa kan kare muhalli karo na 18 da aka gudanar a Jihar Katsina.

Balarabe Lawal ya ce wannan umarni na cikin wata sabuwar dokar zartarwa ta shugaban ƙasa wadda aka ɗauka domin dakile sare itatuwa ba bisa ƙa’ida ba da kuma lalacewar gandun daji a sassan ƙasar.

Ministan ya jaddada cewa gandun dajin Najeriya na da matuƙar muhimmanci wajen ɗorewar muhalli, domin suna samar da iska da ruwa masu tsafta da tallafa wa hanyoyin samun abin rayuw da, kare nau’o’in halittu, da rage illar sauyin yanayi.

Ya kuma yi gargaɗi cewa ci gaba da fitar da itace zuwa ƙasashen waje na barazana ga waɗannan fa’idodi da kuma lafiyar muhalli a nan gaba.

Dokar wadda aka fitar ta dogara ne da sashe na 17(2) da 20 na ƙundin tsarin mulki na 1999 (da aka yi wa gyara), waɗanda ke bai wa gwamnati ikon kare muhalli da gandun daji da namun daji, tare da hana cin gajiyar albarkatun ƙasa don amfanin ƙashin kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp