Home Labarai Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci majalisar dattawar ƙasar ta amince da naɗin Engr Saidu Aliyu Mohammed, a matsayin sabon shugabannin Hukumar Kula da Albakatun mai na kan tudu NMDPRA, bayan murabus daga matsayin da Engr Farouk Ahmed ya yi.

A cikin wata sanarwa da mai taimakawa shugaba Tinubu wajen hulda da kafafen yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ta ce shugaban ya kuma nemi majalisar ta amince ya naɗa Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan, a matsayin magajin Gbenga Komolafe, da ke shugabantar hukumar kula da albarkatun mai na cikin ruwa.

Tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari ne ya naɗa su a shekarar 2021, domin jagorantar hukumomin biyu da dokar masana’antar mai ta ƙasar ta ƙirƙiro.

Wannan dai na zuwa ne bayan da a ranar lahadin da ta gabata, shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote, Aliko Dangote ya zargin Engr Farouk Ahmed da biya wa ƴaƴansa 4 kuɗin makaranta a Switzerland, da suka kai dala miliya biyar.

Tuni dai hukumar yaƙi da almundahana ta ICPC a Najeriya, ta tabbatar da karɓar ƙorafin da Ɗangote ya shigar gabatanta, kuma ta ce za ta yi bincike akai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp