Home Labarai Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci majalisar dattawar ƙasar ta amince da naɗin Engr Saidu Aliyu Mohammed, a matsayin sabon shugabannin Hukumar Kula da Albakatun mai na kan tudu NMDPRA, bayan murabus daga matsayin da Engr Farouk Ahmed ya yi.

A cikin wata sanarwa da mai taimakawa shugaba Tinubu wajen hulda da kafafen yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ta ce shugaban ya kuma nemi majalisar ta amince ya naɗa Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan, a matsayin magajin Gbenga Komolafe, da ke shugabantar hukumar kula da albarkatun mai na cikin ruwa.

Tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari ne ya naɗa su a shekarar 2021, domin jagorantar hukumomin biyu da dokar masana’antar mai ta ƙasar ta ƙirƙiro.

Wannan dai na zuwa ne bayan da a ranar lahadin da ta gabata, shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote, Aliko Dangote ya zargin Engr Farouk Ahmed da biya wa ƴaƴansa 4 kuɗin makaranta a Switzerland, da suka kai dala miliya biyar.

Tuni dai hukumar yaƙi da almundahana ta ICPC a Najeriya, ta tabbatar da karɓar ƙorafin da Ɗangote ya shigar gabatanta, kuma ta ce za ta yi bincike akai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp