‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar OOU
Jihar Ogun, Nigeria – Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun kai hari dakunan kwanan dalibai a Jami’ar Olabisi Onabanjo (OOU) da ke Ibogun a jihar Ogun.
Rahotanni sun nuna cewa maharan sun bude wuta daga shiga cikin gidan kwanan da tsakar daren jiya Juma’a, lamarin da ya jefa dalibai cikin firgici yayin da suka rika guduwa domin tsira.
Mahara sun bude wuta a dakunan kwana Rahotan jaridar The Nation ya ce harin ya fara ne da tsakar dare, ya kuma ci gaba har zuwa safiyar Asabar, inda sama da mutane 12 dauke da makamai suka shiga dakunan kwanan dalibai da dama.
An ce maharan sun rika harbe-harbe domin tsoratar da dalibai kafin su kwashe wayoyi, kwamfutoci da sauran kayayyaki masu daraja.
Yadda daliban OOU suka shiga firgici
Read Also:
Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Michael Mabayomije, ya bayyana cewa maharan sun yi aiki na tsawon lokaci ba tare da jami’an tsaro sun kai dauki ba.
Ya ce dalibai da dama sun jikkata a harin, yayin da wasu kuma suka shiga matsanancin firgici saboda tashin hankalin da suka gani.
Jaridar Punch ta kuma rawaito cewa an ga jini a bango da bene na daya daga cikin gidajen kwanan dalibai da abin ya shafa.
Mazauna Ibogun sun bayyana lamarin a matsayin mai tayar da hankali, inda suka ce karar bindiga ta karade harabar jami’ar yayin da dalibai ke kokarin tserewa domin ceton rayuwarsu
Wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun samu raunuka yayin da suke kokarin gudu ko kuma tsayawa kare kansu.
Wane mataki yan sanda suka dauka?
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Oluseyi Babaseyi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce tuni jami’ai suka kaddamar da bincike kan lamarin.
Ya ce an fara bincike kan harin, tare da tura jami’an tsaro ciki har da DPO na yankin Ibogun da kuma kwamandan da ke kula da yankin domin duba halin da ake ciki da kuma kwantar da hankalin dalibai da mazauna yankin.












