Home DUNIYA Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar...

Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar Rigakafin Corona ba – Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya

Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar Rigakafin Corona ba – Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya

 

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce kashi 80 cikin 100 na mutanen Afirka har yanzu ba a yi musu allurar riga-kafin corona ko da ɗaya ba.

Dr Tedros ya bayyana hakan ne a lokacin wani taro ta intanet yayin cika shekara daya da kaddamar da shirin samar da rigakafin a duniya da ake kira Covax.

Ya ce “kiyasinmu ya nuna cewa riga-kafin da za a samar za ta isa a yi wa dukkanin manya na duniya kuma har a kara yi wa mutanen da ke cikin hadarin kamuwa da cutar sosai zuwa wata uku na farkon shekaran nan”.

Covax shiri ne na tabbatar da raba daidai a tsakanin kasashen duniya wajen samar da riga-kafin corona.

Shugaban na WHO ya ce shirin ya gamu da nakasu sosai saboda abin da ya kira “kaka-gida” da kasashe suka yi a kan rigakafin da kuma yadda kamfanonin da ke samar da ita suka fi bayar da fifiko ga kasashe masu karfin arziki.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp