Home Labarai ‘Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari...

‘Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta

‘Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta

Daya daga cikin motocin da ke cikin ayarin shugaban ma’aikatan Buhari, Ibrahim Gambari, da minista Fashola da takwaransa Ngige sun yi hatsari a Asaba, jihar Delta.

‘Yan sanda hudu ne ake fargabar sun mutu a hatsarin wanda aka ce ya faru ne da yammacin ranar Talata, 8 ga watan Maris.

Rahotanni sun ce manyan jami’an gwamnatin sun je babban birnin jihar Delta ne domin duba wata gada da aka gina.

Asaba, jihar Delta – Ayarin shugaban ma’aikata, Ibrahim Gambari; Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola; da takwaransa na ma’aikatar kwadago da samar da aikin yi, Christ Ngige, sun yi hatsari a yammacin ranar Talata, 8 ga watan Maris.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa hatsarin ya afku ne a yayin duba wata gada a garin Asaba na jihar Delta, inda rahoton ya kara da cewa ‘yan sanda hudu ne ake fargabar sun mutu.

An tattaro cewa direban motar ne ya rude yayin tuka motar da ke dauke da jami’an tsaro inda ta fada cikin wani rami mai zurfi.

Shaidun gani da ido sun bayyana yadda lamarin ya faru

Wani shaidan gani da ido, John Okorie, ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da motar da ke dauke da wadanda lamarin ya rutsa dasu ke tattaunawa kan kwanar da ta kai ga wajen aikin gina gadar Neja ta biyu a Asaba.

An tattaro cewa motar ‘yan sandan ta yi gudu ne don haduwa da sauran tawagar motocin ministocin ne a lokacin da ta kauce daga titi kuma ta yi hatsari.

Har ila yau, wani direba a Delta, wanda bai bayyana sunansa ba, ya ce:

“Lamarin ya yi muni matuka.

“Direba dan sandan yana gudu yayin da ake tattaunawa kan lankwasar hanyar wanda saboda gudun ya kasa sarrafa motar. Suka fada cikin wani rami mai zurfi. Ni ina bin bayan ayarin, ina tuki na a hankali.

“Da taimakon wasu mutane mun ceto hudu daga cikinsu amma sun samu munanan raunuka. Suna ta ihu yayin da motar ta fado musu.”

Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe, ya ce har yanzu bai samu rahoton faruwar hatsarin ba.

Karin bayani nan tafe…

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp