Home Labarai Fadan Daba: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta Haramta Tashe

Fadan Daba: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta Haramta Tashe

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta haramta Al’adar nan ta tashe a Jihar.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ranar Litinin.

“Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano karkashin jagorancin kwamishinan ta CP Sama’ila Sha’aibu Dikko na sanar da al’ummar Jihar Kano cewa, a dakata da gudanar da Al’adar nan ta tashe, wadda ake yin ta daga 10 ga wata Azumin Ramadana, wannan ya biyo bayan fakewa da wasu bat a garin matasa ke yi da tashen suna fadan daba, kwacen waya da kuma ta’ammali da miyagun kwayoyi”.

SP Kiyawa ya yi kira ga iyaye da su tabbatar basu bar ‘Ya’yansu sun karya doka ba, domin kuwa duk wanda aka kama ya karya doka, ba shakka doka zatayi aiki akan shi.

Bisa al’ada, idan azumin watan Ramadan yakai kwanaki 10, akwai al’adar Tashe da kuma kidan gwauro da ake gudanarwa a kasar Hausa, wanda a wannan shekarar hukumar yan sanda ta jihar Kano, tace babu bukatar hakan, kuma tayi gargadi mai zafi ga duk wanda ya fito ya aiwatar da hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp