Home Labarai Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

President-Muhammadu-Buhari

 

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba da umarnin cewa a gaggauta sakin tan 40,000 na kayan Abinci daga asusun ajiyar hatsi na Gwamnatin Tarayya, domin taimakawa marasa karfi a yayin gudanar da bukukuwan Easter da sallah.

Ministan Noma da Raya Karkara Muhammed Mahmoud ne ya bayyana hakan a yayin da yake ganawa da manema labarai na Fadar Shugaban Kasa bayan wata ganawar sirri da Shugaba Muhammadu Buhari a fadar sa dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata.

Mahmood, yace Shugaba Buhari ya bashi umarnin raba kayayyakin ga Al’ummar Nijeriya, ya kuma bayyana cewa yana fatan rabon kayan abincin zai ragewa Al’umma radadin hauhawar farashin kayan masarufi.

Ya kara da cewa, ton dubu 12 daga cikin dubu 40 da aka amince dasu za’a baiwa ma’aikatar kula da jin kai da bala’oi da ci gaban jama’a ta tarayya domin rabawa ‘yan gudun hijira a fadin kasar nan.

Economic Confidential ta rawaito ministan na cewa za’a yi amfani da tsarin da aka bi a lokacin kullen Corona (covid-19) a shekarar 2020, wajen raba ton dubu 70 na kayan abinci a wasu jihohin ciki har da birnin tarayya Abuja.

“Idan dai zaku iya tunawa, lokacin kullen corona a kasar nan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin fidda hatsi domin rabawa masu karamin karfi a Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp