Home Labarai Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na jagorantar taron Majalisar Magaba a fadar Aso Rock dake birnin tarayya Abuja ranar Alhamis.

PRNigeria ta hangi Tsoffin Shugabannin Nijeriya da suka hadar da Janar Abdulsammi Abubakar (rtd) Dr. Goodluck Jonathan, da kuma Janar Yakubu Gowon (rtd), taron da aka fara karfe goma an gudanar da shine a zahiri da kuma kafar internet.

Wannan shine karo na hudu da shugaban ke jagorantar taron. An gudanar da taron farko ne a ranar 21 ga Oktoban, 2015, inda aka gudanar da karon na biyu ranar 7 ga Satumbar 2016 yayin da karo na uku ya kasance a watan August 2020.

Haka kuma sauran wadanda suka sami halartar taron sun hadar da Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo, Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha, Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara a sabgar tsaro Babagana Monguno, da kuma Shugaban Ma’aikatar Fadar Shugaban Kasa Farfesa Ibrahim Gambari.

Gwamnonin da suka sami halartar taron sun hadar da Gwamnan Jihar Imo Hope Uzodinma, Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi, Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu, Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle sai kuma Gwamnan jihar Kaduna Nasir El’Rufa’i.

Kafin fara taron Majalisar Magabatan tayi shiru na minti daya don girmama ga tsohon shugaban Gwamnatin rikon kwarya, Earnest Shonekan, wanda ya rasu a 11 ga watan janairun 2022.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp