Home Labarai TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso...

TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso Gabas

A wani yunkuri na kawo cikas ga nasarorin da Dakarun Sojin Nijeriya ke samu akan mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, mayakan sun dauki salon dasa bama bamai a kan manyan hanyoyin dake yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya.

PRNigeria ta gano cewa mutane da dama sun rasa rayukan su sakamakon tarwatsewar wasu nakiyoyi mafi akasarin su kirara gida da ‘yan bindigar suka binne.

Wani bincike da PRNigeria ta gudanar Ya bayyana cewa yankunan da ‘Yan da ta’addan suka binne abubuwan fashewar sun hadar da Maiduguri, Damboa, Biu, Bama, Banki, Gwoza, Buni Yadi, Malam Fatori da Kukawa.

Majiyoyin jami’an tsaro sun shaida cewa za’a dauki tsawon lokaci kafin sojoji su kammala kunce nakiyoyin dake binne a karkashin kasar.

Ko a ‘yan tsakanin nan kwamandan Operation Hadin Kai Manjo Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa gano bazuwar bama-baman babban kalubale ne a yakin da Rundunar ke yi da masu tayar da kayar baya a yankin.

Inda yace “Dakarun Sojin sai sun bincika ko ina kafin su gudanar da ayyukan su na kakkabe ‘yan ta’addan a ko ina, sannan sai sun sake bincikawa a hanyar su ta dawowa.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp