Home Labarai Dakarun ‘Yan Sanda Sun Lakadawa Kwamandan Hukumar NSCDC Duka

Dakarun ‘Yan Sanda Sun Lakadawa Kwamandan Hukumar NSCDC Duka

Dakarun Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Imo dauke da Makamai, sun kutsa shalkwatar hukumar tsaro ta Civil Defence (NSCDC) inda suka lakadawa kwamandan hukumar Micheal Ogar dukan kawo wuka.

Rahotan da PrNigeria ta samu ya nuna cewa tuni jami’an ‘Yan Sandan suka halaka mai tsaron lafiyar Kwamandan, bayan da Dakarun Hukumar ta Civil Defence ke kwance cikin muggana raunika.

PRNigeria ta rawaito cewa jami’an ‘Yan Sandan Kwantar da tarzo ta Mobile Police na Squadron – 18 a Jihar ta Imo ne suka aika ta wannan danyen hukunci.

Lamarin dai ya faru ne bayan da kwamandan ya shiga tsakanin wata takaddama daga auku tsakanin jami’in hukumar da wasu jami’an ‘Yan sanda.

Wata sahihiyar majiya ta shaidawa PRNigeria cewa lamarin ya faru tsakanin jami’an inda aka dingi musayar wuta da manyan bindigu a shalkwatar hukumar ta NSCDC dake kusa works layout a Owerri, Babban Birnin Jihar.

Binciken da PrNigeria ta gudanar ya nuna cewa rikicin ya samu asali ne bayan takaddama  mai zafi tsakanin direban kwamandan Hukumar ta NSCDC na  Jihar ta Imo da wani Dan Sanda a kayan gida wanda ya rufe hanyar da kwamandan zai wuce.

Har zuwan lokacin hada wannan rahoto, PRNigeria bata sami nasarar jin ta bakin Kakakin hukumomin guda biyu ba

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp