Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Tabbatar da Mutum 7 Sakamakon Harin ‘Yan Bindiga A Jihar

A kalla mutum 7 ne suka mutu sakamakon harin ‘Yan bindiga a kauyen Kurfi dake karamar hukumar Takai a jihar Kano.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da Dagacin Garin tare da raunata Mutum 3 a yayin harin.

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyanawa manema labarai cewa tuni hukumar ‘Yan sandan jihar ta tura jami’an ta domin bin sahun ‘yan bindigar.

Wani shaidar gani da Ido Sale Hussaini ya bayyanawa PRNigeria cewa, ‘yan bindigar sun kaddamar da harin ranar Asabar daakrfe 11 dare, inda kai tsayi suka durfafi gidan mai Gari.

Ya bayyana sunan Dagacin Kauyen da Abdul-hayatu Ilu, inda yace guda cikin wadanda aka kashe makoci ne ga mai rike da sauatar gargajiyar.

‘Yan bindigar kuma suna halaka mutum 5 garin Tudun Makama dake makotaka da kauyen, bayan da AL’umma suka bi bayan ‘yan bindigar.

Ya kuma bayyana sunayen wadanda ‘yan bindigar suka halaka da suka hadar da Tasi’u Birniyo, Ali Yahaya, Hashimmu Amo, Sadiq hussaini, Ahmadu danlanbu, bala Audu da kuma Shu’aibu Agwar-maji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp