Home Labarai Yadda Iyalan Sheik Agaka Suka Bawa Iyalai Na Ilimin Addinin Musulunci, “Sulu...

Yadda Iyalan Sheik Agaka Suka Bawa Iyalai Na Ilimin Addinin Musulunci, “Sulu Gambari”

Mai Martaba Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu Gambari, ya bayyana Marigayi Dr. Abdulhameed Shuaib Agaka matsayin mai kyakkyawan halaye da riko da addini.

Sheik Agaka, Mahaifi ga mawallafin jaridar PRNigeria kuma babban mai tace labarai, Yusha’u Shuaib, ya rasu a ranar Asabar, yana da shekaru 77 a duniya.

Agaka fitacce malamin Addinin muslunci kuma babban limamin garin Agaka dake masarautar Ilorin ta Jihar Kwara, ya rasu ne a wani asibiti mai zaman kansa dake garin, bayan yayi fama da gajeruwar rashin lafiya.

Haka zalika yana da digirin digirgir a fannin falsafa, an haife shi a cikin dangin Imam Shuaib Saeed, wani mashahurin malami masanin Al’kurani kuma jagoran addini musulunci.

Mai Martaba sarkin Ilorin Sulu Gambari ya bayyana matukar kaduwarsa bisa ga rasuwar mahaifin mawallafin jaridar ta PRNigeria, yayi da ya karbi bakuncin tawagar Iyalan marigayin, a fadarsa, a ranar litinin.

Mai martaba sarkin ya kuma jajantawa tawagar iyalan marigayin bisa jagorancin Dawudu Agaka, Alh. Hanafi Folorunsho Kawu, da daukacin  iyalan Malamin bisa rashin da suka yi na hazaki, kuma cikakken Mutum mai adalci marashin aibi.

Sarkin bayyana cewa Al’ummar jihar kwara da kasa baki daya sunyi gagarumin rashi na malamin Addini da baza a iya misalta rashin ba.

Sarkin na Ilorin ya kara da cewa Iyalan Sheik Agaka, na da alaka da masu yawon yada addinin Musulunci “masu wa’azi” tsawon shekaru da dama a Nijeriya, kasancewar marigayu Abdulhameed ya kasance daya daga cikin manayan malaman addinin muslunci da masarautar ta samar.

Dr. Sulu Gambari, yace ya amfana matuka da wa’azin sheik Abduhameed, inda yace mahaifiyar sa ta kuma shafe shekarunta tana karatu al’kurani a wajen Sheik Agaka.

Tun bayan samun labarin mutuwar Sheik Agaka manayan malamai gami da masu rike da sarautun gargaji, da ‘yan takarda sun nuna kaduwar su matuka tare da Addu’ar Allah yayi masa rahama yasa Aljanna ce makoma ya kuma inganta abinda ya bari.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp