Home Labarai Dakarun Sojin Sama Sun Halaka Mayakan ISWAP 13 Tare da Kama 5

Dakarun Sojin Sama Sun Halaka Mayakan ISWAP 13 Tare da Kama 5

Dakarun sojin saman Nijeriya sun sami nasarar halaka mayakan kungiyar Boko Haram tsagin ISWAP, a yakin Arewa Maso Gabashin kasar kamar yadda PRNigeria ta rawaito.

Mayakan da dakarun suka halaka da sanyin safiyar Litinin sun sanya shingen tsare ababa hawa a hanyar  Goni Masari dake kusa da hanayar Maiduguri zuwa Damaturu, a jihar Borno.

Dakarun rundunar sojin  sun sami wani rahoton sirri daya bayyana yadda mayakan suka tare kan hanyar wanda tuni har sun sami damar yin garkuwa da wani matukin mota, nan basuyi kasa a gwuiwa ba suka farmake su da jiragen yaki.

A cewar kwmandan daya jagoranci kai harin yace dakarun sojin sun sami nasarar kubutar da wanda akayi garkuwa dasu su 5, a harin da suka kai wa ‘yan ta’addan.

Kwamandan, wanda ya ki bayyana sunansa ga PRNigeria, yace sojojin sun halaka mayakan kungiyar ta ISWAP sama da 13, tare da raunata wasu da dama, inda suka sami nasarar kwato motar dake dauke da bindiga da suka bari a wajen.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp