Home Labarai ‘Yan Sanda Sun Halaka ‘Yan Ta’adda Tare Da Kama Wadda Ke Musu...

‘Yan Sanda Sun Halaka ‘Yan Ta’adda Tare Da Kama Wadda Ke Musu Safarar Makamai A Kaduna

Dakarun rundunar yan sandan Nijeriya ta musamman dake birnin tarayya Abuja hadin gwuiwa da Dakarun Operation Yaki sun sami nasarar halaka ‘yan Ta’adda guda 4 tare da kame wata mata dake musu safarar Alburusai akan babbar hanyar Saminaka zuwa Jos a Jihar Kaduna.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar DSP Mohammed Jalige ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da aka rana ga manema labarai, sanarwar tace lamarin ya auku ne ranar laraba 15 ga watan Yuni, yayi da ‘yan sandan suka kama ‘yan bindigar cikin wata shudiyar mota (blue) wadda James Dawi mai kimanin shekaru 31 dan asalin garin Vom na karamar hukumar Jos ta kudu a Jihar Plateau.

Sanarwa ta kara da cewa maharani sun gamu da gamon su a hanayar su ta kai wasu muggana makamai ga tawagarsu, inda suka yi musayar wuta da jami’an.

“kwararrun Jami’an sun sami nasarar raunata wasu mutane 4 da ake zargi. Yayin da aka garzaya da su asibitin koyarawa na Barau Dikko dake Kaduna, inda likitoci suka tabbatar da mutuwar su, said ai ya tabbatar da cewa wasu cikin ‘yan bindiga sun tsere daji da raunukan harbi a cikin su.

Ya kara da cewa yayin da dakarun ke gudanar da bincike a cikin motar, an gano bindiga kirar AK49 guda 1dauke da alburusai guda 6, tare da wani kwanson masakin alburushin, da kuma wasu tarin Alburusai guda 134 da kuma wata mota guda 1.

Yace dakarun a yayin atisayen sun kuma kama wata mata, wadda da ake gudanar da bincike ta amsa cewa ita ke yiwa ‘yan bindigar safarar makamai a jihar Kaduna.

Daga bisani ya bayyana cewa hanzu haka dai hukumar ‘yansandan jihar na zurfafa bincike kan lamarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp