Home Labarai Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun...

Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun ‘Yan Ta’adda

Train attack: Reps ask Buhari to secure release of remaining 51 kidnapped victims

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci shugaban kasar Muhammadu Buhari daya gaggauta daukar matakin ganin an sako sauran fasinjoji 51 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a a wani yarin jirgin kasan Abuja zuwa Kano.

Har ila yau, majalisar ta bukaci gwamnatin tarayya ta kafa wani kwamiti mai karfi don ganin an kubutar da wadanda ke hannun ‘yan bindigar, dadukkan wadanda ke hannun ‘yan bindigar a fadin kasar, gami da bayar da taimako ga iyalan wadanda aka yi garkuwa da su.

Wanna bukata ta majalisar ta biyo bayan Nazari kan wani kudiri da Bamidele Salam da wasu ‘yan majalisar su 10 suka gabatar a zauren majalisar.

PRnigeria ta rawaito Dan majalisar Salam Ya gudanar da wani tattaki shi kadai a kwaryar birnin tarayya, wanda ya bukaci a sako wadanda akayi garkuwa dasu.

Cikin kudirin, dan majalisar ya bayyana cewa sashe na 14 (2) (b) na kundin tsarin mulkin da aka yiwa kwaskwarima 1999, ya bayyana cewa, tsaro da jin dadin jama’a shi ne babbar manufar gwamnati, kamar yadda sashe na 17 (2) (b) na kundin tsarin mulkin kasar ya bayyana muhimmancin dan Adam tare da inganta martabar sa da kare ta.

Ya kara da cewa, tsawon shekaru 10 da suka wuce, ta’addanci, ‘yan fashi masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, gami da munana laifuka sun zamo annoba ga tsaron kasar a sassa daban-daban na kasar.

Da take amincewada kudirin, majalisar wakilan ta umarci dukkanin kwamitocin da abin ya shafa na majalisar da su tabbatar da aiki da kudirin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp