Home Labarai Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun...

Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun ‘Yan Ta’adda

Train attack: Reps ask Buhari to secure release of remaining 51 kidnapped victims

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci shugaban kasar Muhammadu Buhari daya gaggauta daukar matakin ganin an sako sauran fasinjoji 51 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a a wani yarin jirgin kasan Abuja zuwa Kano.

Har ila yau, majalisar ta bukaci gwamnatin tarayya ta kafa wani kwamiti mai karfi don ganin an kubutar da wadanda ke hannun ‘yan bindigar, dadukkan wadanda ke hannun ‘yan bindigar a fadin kasar, gami da bayar da taimako ga iyalan wadanda aka yi garkuwa da su.

Wanna bukata ta majalisar ta biyo bayan Nazari kan wani kudiri da Bamidele Salam da wasu ‘yan majalisar su 10 suka gabatar a zauren majalisar.

PRnigeria ta rawaito Dan majalisar Salam Ya gudanar da wani tattaki shi kadai a kwaryar birnin tarayya, wanda ya bukaci a sako wadanda akayi garkuwa dasu.

Cikin kudirin, dan majalisar ya bayyana cewa sashe na 14 (2) (b) na kundin tsarin mulkin da aka yiwa kwaskwarima 1999, ya bayyana cewa, tsaro da jin dadin jama’a shi ne babbar manufar gwamnati, kamar yadda sashe na 17 (2) (b) na kundin tsarin mulkin kasar ya bayyana muhimmancin dan Adam tare da inganta martabar sa da kare ta.

Ya kara da cewa, tsawon shekaru 10 da suka wuce, ta’addanci, ‘yan fashi masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, gami da munana laifuka sun zamo annoba ga tsaron kasar a sassa daban-daban na kasar.

Da take amincewada kudirin, majalisar wakilan ta umarci dukkanin kwamitocin da abin ya shafa na majalisar da su tabbatar da aiki da kudirin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp