Home Labarai Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun...

Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun ‘Yan Ta’adda

Train attack: Reps ask Buhari to secure release of remaining 51 kidnapped victims

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci shugaban kasar Muhammadu Buhari daya gaggauta daukar matakin ganin an sako sauran fasinjoji 51 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a a wani yarin jirgin kasan Abuja zuwa Kano.

Har ila yau, majalisar ta bukaci gwamnatin tarayya ta kafa wani kwamiti mai karfi don ganin an kubutar da wadanda ke hannun ‘yan bindigar, dadukkan wadanda ke hannun ‘yan bindigar a fadin kasar, gami da bayar da taimako ga iyalan wadanda aka yi garkuwa da su.

Wanna bukata ta majalisar ta biyo bayan Nazari kan wani kudiri da Bamidele Salam da wasu ‘yan majalisar su 10 suka gabatar a zauren majalisar.

PRnigeria ta rawaito Dan majalisar Salam Ya gudanar da wani tattaki shi kadai a kwaryar birnin tarayya, wanda ya bukaci a sako wadanda akayi garkuwa dasu.

Cikin kudirin, dan majalisar ya bayyana cewa sashe na 14 (2) (b) na kundin tsarin mulkin da aka yiwa kwaskwarima 1999, ya bayyana cewa, tsaro da jin dadin jama’a shi ne babbar manufar gwamnati, kamar yadda sashe na 17 (2) (b) na kundin tsarin mulkin kasar ya bayyana muhimmancin dan Adam tare da inganta martabar sa da kare ta.

Ya kara da cewa, tsawon shekaru 10 da suka wuce, ta’addanci, ‘yan fashi masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, gami da munana laifuka sun zamo annoba ga tsaron kasar a sassa daban-daban na kasar.

Da take amincewada kudirin, majalisar wakilan ta umarci dukkanin kwamitocin da abin ya shafa na majalisar da su tabbatar da aiki da kudirin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp