Home Labarai ‘Yan Sanda Sun Halaka ‘Yan Ta’adda Tare Da Kama Wadda Ke Musu...

‘Yan Sanda Sun Halaka ‘Yan Ta’adda Tare Da Kama Wadda Ke Musu Safarar Makamai A Kaduna

Dakarun rundunar yan sandan Nijeriya ta musamman dake birnin tarayya Abuja hadin gwuiwa da Dakarun Operation Yaki sun sami nasarar halaka ‘yan Ta’adda guda 4 tare da kame wata mata dake musu safarar Alburusai akan babbar hanyar Saminaka zuwa Jos a Jihar Kaduna.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar DSP Mohammed Jalige ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da aka rana ga manema labarai, sanarwar tace lamarin ya auku ne ranar laraba 15 ga watan Yuni, yayi da ‘yan sandan suka kama ‘yan bindigar cikin wata shudiyar mota (blue) wadda James Dawi mai kimanin shekaru 31 dan asalin garin Vom na karamar hukumar Jos ta kudu a Jihar Plateau.

Sanarwa ta kara da cewa maharani sun gamu da gamon su a hanayar su ta kai wasu muggana makamai ga tawagarsu, inda suka yi musayar wuta da jami’an.

“kwararrun Jami’an sun sami nasarar raunata wasu mutane 4 da ake zargi. Yayin da aka garzaya da su asibitin koyarawa na Barau Dikko dake Kaduna, inda likitoci suka tabbatar da mutuwar su, said ai ya tabbatar da cewa wasu cikin ‘yan bindiga sun tsere daji da raunukan harbi a cikin su.

Ya kara da cewa yayin da dakarun ke gudanar da bincike a cikin motar, an gano bindiga kirar AK49 guda 1dauke da alburusai guda 6, tare da wani kwanson masakin alburushin, da kuma wasu tarin Alburusai guda 134 da kuma wata mota guda 1.

Yace dakarun a yayin atisayen sun kuma kama wata mata, wadda da ake gudanar da bincike ta amsa cewa ita ke yiwa ‘yan bindigar safarar makamai a jihar Kaduna.

Daga bisani ya bayyana cewa hanzu haka dai hukumar ‘yansandan jihar na zurfafa bincike kan lamarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp