Home Labarai Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hukumar kiyaye Aukuwar hadurra reshen jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar mutum 7 kuma mutum 5 sun jikkata, yayin da wasu motoci 2 sukayi taho mu gama a kan babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja a ranar Alhamis.

Kwamandan shiyya na na hukumar ta FRSC, Stephen Dawulung ne ya tabbatar aukuwar lamarin ga manema labarai a garin lokoja ranar Juma’a.

Yace lamarin ya faru ne yayi da wata mota Bus kirar Toyota Hiece tayi gaba da gaba da wata mota kirar Daf a garin Akpanya dake daura da koton karfe a hanyar Abuja zuawa lokoja.

“yayin da motocin 2 sukay taho mu gama, mutum 7 suka mutu nan take, inda mutum 5 kuma suka sami raunika a sassan jikin su.

“Jami’an mu sun garzawa wajen da lamarin ya faru bayan samun rahoto, nan suka shiga ikin taimako nan kuwa suka taimaki musamman wadanda suka ji rauni da taimakon gaggawa.

“tuni dai an garzaya da wadanda suka ji raunin zuwa asibitin koton karfe, inda ake lura da lafiyar tasu, an kuma an ajje wadanda suka mutu a warin ajiyar gawarwaki na asibiti (Mortuary) kamar yadda ya bayyana.

Dawulung ya bayyana cewa hadarin ya auku ne sakamakon Gudun wuce sa’a da matuka Ababan hawan ke yi a yayin da suke tsaka da tuki.

Daga bisani ya bukaci Al’umma, musamman matuka Ababan hawa da su gujewa tafiyar dare, tare da yin gudun wuce sa’a, yayin tukun kuma su tabbatar sun bi dokoki da ka’idojin hanya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp