Home Labarai Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hukumar kiyaye Aukuwar hadurra reshen jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar mutum 7 kuma mutum 5 sun jikkata, yayin da wasu motoci 2 sukayi taho mu gama a kan babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja a ranar Alhamis.

Kwamandan shiyya na na hukumar ta FRSC, Stephen Dawulung ne ya tabbatar aukuwar lamarin ga manema labarai a garin lokoja ranar Juma’a.

Yace lamarin ya faru ne yayi da wata mota Bus kirar Toyota Hiece tayi gaba da gaba da wata mota kirar Daf a garin Akpanya dake daura da koton karfe a hanyar Abuja zuawa lokoja.

“yayin da motocin 2 sukay taho mu gama, mutum 7 suka mutu nan take, inda mutum 5 kuma suka sami raunika a sassan jikin su.

“Jami’an mu sun garzawa wajen da lamarin ya faru bayan samun rahoto, nan suka shiga ikin taimako nan kuwa suka taimaki musamman wadanda suka ji rauni da taimakon gaggawa.

“tuni dai an garzaya da wadanda suka ji raunin zuwa asibitin koton karfe, inda ake lura da lafiyar tasu, an kuma an ajje wadanda suka mutu a warin ajiyar gawarwaki na asibiti (Mortuary) kamar yadda ya bayyana.

Dawulung ya bayyana cewa hadarin ya auku ne sakamakon Gudun wuce sa’a da matuka Ababan hawan ke yi a yayin da suke tsaka da tuki.

Daga bisani ya bukaci Al’umma, musamman matuka Ababan hawa da su gujewa tafiyar dare, tare da yin gudun wuce sa’a, yayin tukun kuma su tabbatar sun bi dokoki da ka’idojin hanya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp