Home Labarai Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma (NANNM) ta Bukaci Adalci

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma (NANNM) ta Bukaci Adalci

Kungiyar ma’aikatan jinya da Ungozoma ta kasa (NANNM), reshen birnin tarayya Abuja, ta bukaci a yi adalci bisa cin zarafin da akayi kan mambarta Abalu Marvis ta asibitin kasa dake Abuja.

Shugabar kungiyar, kwared Deborah Yusuf ce ta bayyana hakan yayin da take ganawa da manema labarai a ranar juma’a, inda tayi zargin cewa Dr. Atinko-Sunday Ikeya na asibiti ya afkawa Marvis yayin da take tsaka da lura da marasa lafiya.

Ta kara da cewa a ranar 13 ga watan yuni, Ikeyi yayi fatali da duk wata ka’ida ta aikin likitanci da ya kuma yi amfani da damar wajen cin zarafin ma’aikaciyar jinyar dake tsaka da aiki a matsayin abokiyar aikin sa.

Debora Yusuf tace, Jami’ar jinyar da likitan ya wulakanta, na tsaka da kula da wani mara lafiyar, likitan yace lallai sai ta bar wannan ta koma kan wanda ya uwace ta, wannan ya sanya har ta kai ga yaci zarafin ta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp