Home Labarai ‘Yan Bindiga Sunyi garkuwa Da DPO A Jihar Kaduna

‘Yan Bindiga Sunyi garkuwa Da DPO A Jihar Kaduna

‘Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kama sabon baturen ‘yan sanda da aka tura karamar hukumar birnin Gwari dake jihar kaduna.

Anyi garkuwa da baturen ‘yan sandan ne akan babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari da misalin karfe 9 na safiyar ranar litinin a yayin da yake kokarin zuwa inda aka turashi domin kama aiki.

Wata majiya ta sai dawa PRNigeria cewa baturen ‘yan Sandan (DPO) na kan hanyar sa zuwa birnin Gwari masu garkuwar suka kama shi, sai kawo yanzu ba’a tabbatar da ko yayi tafiya shi kadai bane ko akasin haka.

Kawo yanzu dai hukumar ‘yan sandan jihar na tattara bayanai domin fidda sanarwa a hukumance, kamar yadda kakakin Rundunar ‘yan sandan jihar ta Kaduna Muhammad Jalige ya bayyana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp