Home Labarai Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta ICPC ta gurfanar da mataimakin kwamandan hukumar dake bada kariya ga fararen hula ta Civil Defence Mr Boutidem Akpan gaban kotu kan zarginsa da badakalar kudaden da suka kai naira miliyan 26 da dubu dari 655.
An gurfanar da Mr Akpan gaban mai shari’a V. S. Gaba na babbar kotun tarayya dake Kwali a birnin Abuja ne bisa tuhumarsa da laifuffuka 17 dake da jibi da almundahana da dukiyar kasa, da ya hadar da amfani da sunan kamfaninsa wajen damfara.
Cikin takardar tuhumar dai ta nuna ana zarginsa da amfani da kujerarsa wajen yaudarar wasu mutane ta hanyar karbar kudi daga hannunsu da sunan hukumar, yana mai cewa hukumar ce za ta raba musu filaye a yankin Karshi da Sabon Lugbe da kan titin Filin jirgi da kuma wasu filaye a jihar Nassarawa, wanda kuma kawo yanzu ba a bas u filayen ba.
Hukuar ICPC dai ta shaidawa kotu cewa ya aikata laifukan ne a tsakanin shekarun 2010 zuwa 2015 kuma laifukan sun saba da sashi na 19 da 26 karamin sashi na 1 sakin layi na 3 na kundin dokokin hukumar na shekarar 2000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp