Home Labarai Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Babban hafsan sojin ruwa CNS, Vice Admiral Awwal Zubairu Gambo, ya bayyana farin cikinsa game da yadda PRNigeria ke wallafa labaran da ya shafi sojoji da fannin tsaro ba tare da nuna son rai ba.

Ya bayyana hakan ne ta bakin kakakin rundunar sojojin Ruwan Commodore Adetun Ayo-Vaughan, wanda ya jagoran tawagar jami’an rundunar wata ziyarar kafa da kafa zuwa hedikwatar jaridar dake Birnin tarayya Abuja.

A cewar, PRNigeria zata cigaba da kasancewa kamfanin dillancin labarai na daya kuma taka tabbatar da wallafa da sahihin labari kan ayyukan sojoji da sauran jami’an tsaro.

Yace: PRNigeria ta tabbatarwa da kanta tsayuwa kan gwadaben wallafa labaran gaskiya da gaskiya kan lamurran tsaro musamman sojojin Nijeriya.

Ya kara da cewa sojojin Nijeriya sun yaba da ayyukan PRNigeria. Don haka kakakin rundunar yace akwai bukatar a bunkasa alakar dake akwai tsakanin rundunar da Jaridar ta PRNigeria.

Da yake karbar bakin, babban Editan rukunin jaridun dake karkashin kamfanin Image Merchants Promotion (IMPR) Limited dake mallakin PRNigeria Mal. Yusha’u Shuaib, ya yaba kakakin rundunar sojin Ruwan bisa wannan ziyara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp