Home General Gwamnatin Nijeriya ta Sanya Ranar Litinin Matsayin Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Nijeriya ta Sanya Ranar Litinin Matsayin Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Najeriya ta ayyana Litinin 10 ga watan Oktoba a matsayin ranar hutu don murnar bikin Mauludin Fiyayyen Halitta Annabi Muhammadu (S.A.W).

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwar da Babban Sakataren ma’aikatar cikin gida Dr. Shuaib Belgore ya fitar a madadin Minista cikin gida Ra’uf Aregbesola wadda tayi kira ga ‘yan Najeriya musamman al’ummar Musulmi su guji ayyukan tada tarzoma da rashin bin doka da sauran ayyukan laifi.

Ministan cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, wanda ya sanar da haka a madadin gwamnatin tarayyar Najeriya ya taya al’ummar Musulmi a gida da ƙetare murnar sake ganin wannan biki na bana.

Daga bisani ya gargaɗi duk ‘yan kasar da su rungumi son juna da haƙuri da jure zama da juna da jimiri waɗanda na cikin jerin halayen fiyayyen halitta Annabi Muhammadu, inda ya ƙara da cewa yin hakan zai tabbatar da zaman lafiya da tsaro da zaman tare a Najeriya.

Da yake kira a dakatar da duk wasu halaye da za su kawo rarrabuwar kai a faɗin ƙasar, ministan ya kuma buƙaci duk ‘yan Najeriya da kuma musamman matasa su rungumi ɗabi’un aiki tuƙuru da halayyar zaman ga ‘yan’uwansu bil’adama ba tare da la’akari da bambancin addini ko aƙida ko rukunin jama’a da ƙabila ba.

Aregbesola ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya su kasance masu tunanin yanayin tsaro, kuma su kai rahoton duk wani mutum ko aikace-aikacen da ba su amince da take-takensu ga hukumomin tsaro mafi kusa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp