Home General Gwamnatin Nijeriya ta Sanya Ranar Litinin Matsayin Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Nijeriya ta Sanya Ranar Litinin Matsayin Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Najeriya ta ayyana Litinin 10 ga watan Oktoba a matsayin ranar hutu don murnar bikin Mauludin Fiyayyen Halitta Annabi Muhammadu (S.A.W).

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwar da Babban Sakataren ma’aikatar cikin gida Dr. Shuaib Belgore ya fitar a madadin Minista cikin gida Ra’uf Aregbesola wadda tayi kira ga ‘yan Najeriya musamman al’ummar Musulmi su guji ayyukan tada tarzoma da rashin bin doka da sauran ayyukan laifi.

Ministan cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, wanda ya sanar da haka a madadin gwamnatin tarayyar Najeriya ya taya al’ummar Musulmi a gida da ƙetare murnar sake ganin wannan biki na bana.

Daga bisani ya gargaɗi duk ‘yan kasar da su rungumi son juna da haƙuri da jure zama da juna da jimiri waɗanda na cikin jerin halayen fiyayyen halitta Annabi Muhammadu, inda ya ƙara da cewa yin hakan zai tabbatar da zaman lafiya da tsaro da zaman tare a Najeriya.

Da yake kira a dakatar da duk wasu halaye da za su kawo rarrabuwar kai a faɗin ƙasar, ministan ya kuma buƙaci duk ‘yan Najeriya da kuma musamman matasa su rungumi ɗabi’un aiki tuƙuru da halayyar zaman ga ‘yan’uwansu bil’adama ba tare da la’akari da bambancin addini ko aƙida ko rukunin jama’a da ƙabila ba.

Aregbesola ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya su kasance masu tunanin yanayin tsaro, kuma su kai rahoton duk wani mutum ko aikace-aikacen da ba su amince da take-takensu ga hukumomin tsaro mafi kusa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp