Home Labarai Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Babban hafsan sojin ruwa CNS, Vice Admiral Awwal Zubairu Gambo, ya bayyana farin cikinsa game da yadda PRNigeria ke wallafa labaran da ya shafi sojoji da fannin tsaro ba tare da nuna son rai ba.

Ya bayyana hakan ne ta bakin kakakin rundunar sojojin Ruwan Commodore Adetun Ayo-Vaughan, wanda ya jagoran tawagar jami’an rundunar wata ziyarar kafa da kafa zuwa hedikwatar jaridar dake Birnin tarayya Abuja.

A cewar, PRNigeria zata cigaba da kasancewa kamfanin dillancin labarai na daya kuma taka tabbatar da wallafa da sahihin labari kan ayyukan sojoji da sauran jami’an tsaro.

Yace: PRNigeria ta tabbatarwa da kanta tsayuwa kan gwadaben wallafa labaran gaskiya da gaskiya kan lamurran tsaro musamman sojojin Nijeriya.

Ya kara da cewa sojojin Nijeriya sun yaba da ayyukan PRNigeria. Don haka kakakin rundunar yace akwai bukatar a bunkasa alakar dake akwai tsakanin rundunar da Jaridar ta PRNigeria.

Da yake karbar bakin, babban Editan rukunin jaridun dake karkashin kamfanin Image Merchants Promotion (IMPR) Limited dake mallakin PRNigeria Mal. Yusha’u Shuaib, ya yaba kakakin rundunar sojin Ruwan bisa wannan ziyara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp