Home Labarai Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Babban hafsan sojin ruwa CNS, Vice Admiral Awwal Zubairu Gambo, ya bayyana farin cikinsa game da yadda PRNigeria ke wallafa labaran da ya shafi sojoji da fannin tsaro ba tare da nuna son rai ba.

Ya bayyana hakan ne ta bakin kakakin rundunar sojojin Ruwan Commodore Adetun Ayo-Vaughan, wanda ya jagoran tawagar jami’an rundunar wata ziyarar kafa da kafa zuwa hedikwatar jaridar dake Birnin tarayya Abuja.

A cewar, PRNigeria zata cigaba da kasancewa kamfanin dillancin labarai na daya kuma taka tabbatar da wallafa da sahihin labari kan ayyukan sojoji da sauran jami’an tsaro.

Yace: PRNigeria ta tabbatarwa da kanta tsayuwa kan gwadaben wallafa labaran gaskiya da gaskiya kan lamurran tsaro musamman sojojin Nijeriya.

Ya kara da cewa sojojin Nijeriya sun yaba da ayyukan PRNigeria. Don haka kakakin rundunar yace akwai bukatar a bunkasa alakar dake akwai tsakanin rundunar da Jaridar ta PRNigeria.

Da yake karbar bakin, babban Editan rukunin jaridun dake karkashin kamfanin Image Merchants Promotion (IMPR) Limited dake mallakin PRNigeria Mal. Yusha’u Shuaib, ya yaba kakakin rundunar sojin Ruwan bisa wannan ziyara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp