Home Labarai 2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile...

2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile Jam’iyyun Adawa

Biyo bayan rahotannin da ke cewa gwamnatocin jihohin kasar na kokarin dakile ayyukan zaben jam’iyyun adawa da na ‘yan takararsu, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi Allah-wadai da irin wannan dabi’a, inda ta ce a shirye take ta hukunta jihohin da aka samu irin wannan lamari.

A cewar INEC, dukkan jam’iyyun da za su shiga zabukan 2023 suna da ‘yancin gudanar da yakin neman zabe a dukkan jihohin kasar nan 36.

hukumar ta alakatan hakada Jadawalin Ayyuka na yakin neman zaben 2023 na Jam’iyyun siyasa kamar yadda aka tanada a sashe na 94 (1) na dokar zabe ta 2022.

Don haka hukumar ta gargadi gwamnatocin jihohi da kada su hana sauran jam’iyyun siyasa yakin neman zabe a yankunansu.

Babban sakataren yada labarai na shugaban hukumar ta INEC, Mista Rotimi Oyekanmi, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, ya ce akwai hukuncin da ya saba wa wadannan tanade-tanade kuma doka ba zata sassautawa mutum ba komai girman daraja.

Oyekanmi ya ce dokar ta ce za a raba lokacin iska / sararin kafofin watsa labarai na lantarki da na bugu, na jama’a ko na sirri, za a ba su daidai wa daida tsakanin jam’iyyun siyasa ko ‘yan takara a sa’o’i iri ɗaya na ranar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp