Home Labarai Bagudu: Najeriya na Bukatar Masu Zuba Jari a Duniya don Habaka Tattalin...

Bagudu: Najeriya na Bukatar Masu Zuba Jari a Duniya don Habaka Tattalin Arziki

Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu ya ce Najeriya na bukatar hadin gwiwar zuba jari a duniya domin gina tattalin arzikinta, inda ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu fata na gari duk da kalubalen da kasar ke fuskanta.

Bagudu ya hori ‘yan kasar da kada su yanke kauna ko kuma su karaya game da yadda basussukan kasar ke ciki wanda ka iya zama dalilin da zai sa Al’ummar kasar su yanke tsammani.

Hakan ya zo ne a daidai lokacin da takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya shawarci gwamnan jihar Ekiti mai jiran gado, Biodun Oyebanji, da ya inganta ci gaba ta hanyar gina gadon magabacinsa.

Gwamnonin sun yabawa gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi bisa yadda ya samar da amana tsakaninsa da mutanen Ekiti, ta hanyar gudanar da kyakkyawan shugabanci da ya shafi kowane bangare na tattalin arziki.

Sun yi magana ne a Ado Ekiti, jiya a wani taron kasa da kasa da aka gudanar don karrama Fayemi mai taken: “JKF: A Journey in Leadership”.

Bagudu ya ce, “Hatta manyan kasashe irinsu Amurka, wadanda sun fi Najeriya ci gaban tattalin arziki, sun ma fi Najeriya bashi. Abin da muke bukata yanzu shine saka hannun jari ta hanyar haɗin gwiwar duniya sama da mutane miliyan 200, don gina tattalin arzikinmu da gina jama’armu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp