Home Labarai Bagudu: Najeriya na Bukatar Masu Zuba Jari a Duniya don Habaka Tattalin...

Bagudu: Najeriya na Bukatar Masu Zuba Jari a Duniya don Habaka Tattalin Arziki

Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu ya ce Najeriya na bukatar hadin gwiwar zuba jari a duniya domin gina tattalin arzikinta, inda ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu fata na gari duk da kalubalen da kasar ke fuskanta.

Bagudu ya hori ‘yan kasar da kada su yanke kauna ko kuma su karaya game da yadda basussukan kasar ke ciki wanda ka iya zama dalilin da zai sa Al’ummar kasar su yanke tsammani.

Hakan ya zo ne a daidai lokacin da takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya shawarci gwamnan jihar Ekiti mai jiran gado, Biodun Oyebanji, da ya inganta ci gaba ta hanyar gina gadon magabacinsa.

Gwamnonin sun yabawa gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi bisa yadda ya samar da amana tsakaninsa da mutanen Ekiti, ta hanyar gudanar da kyakkyawan shugabanci da ya shafi kowane bangare na tattalin arziki.

Sun yi magana ne a Ado Ekiti, jiya a wani taron kasa da kasa da aka gudanar don karrama Fayemi mai taken: “JKF: A Journey in Leadership”.

Bagudu ya ce, “Hatta manyan kasashe irinsu Amurka, wadanda sun fi Najeriya ci gaban tattalin arziki, sun ma fi Najeriya bashi. Abin da muke bukata yanzu shine saka hannun jari ta hanyar haɗin gwiwar duniya sama da mutane miliyan 200, don gina tattalin arzikinmu da gina jama’armu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp