Home Labarai 2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile...

2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile Jam’iyyun Adawa

Biyo bayan rahotannin da ke cewa gwamnatocin jihohin kasar na kokarin dakile ayyukan zaben jam’iyyun adawa da na ‘yan takararsu, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi Allah-wadai da irin wannan dabi’a, inda ta ce a shirye take ta hukunta jihohin da aka samu irin wannan lamari.

A cewar INEC, dukkan jam’iyyun da za su shiga zabukan 2023 suna da ‘yancin gudanar da yakin neman zabe a dukkan jihohin kasar nan 36.

hukumar ta alakatan hakada Jadawalin Ayyuka na yakin neman zaben 2023 na Jam’iyyun siyasa kamar yadda aka tanada a sashe na 94 (1) na dokar zabe ta 2022.

Don haka hukumar ta gargadi gwamnatocin jihohi da kada su hana sauran jam’iyyun siyasa yakin neman zabe a yankunansu.

Babban sakataren yada labarai na shugaban hukumar ta INEC, Mista Rotimi Oyekanmi, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, ya ce akwai hukuncin da ya saba wa wadannan tanade-tanade kuma doka ba zata sassautawa mutum ba komai girman daraja.

Oyekanmi ya ce dokar ta ce za a raba lokacin iska / sararin kafofin watsa labarai na lantarki da na bugu, na jama’a ko na sirri, za a ba su daidai wa daida tsakanin jam’iyyun siyasa ko ‘yan takara a sa’o’i iri ɗaya na ranar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp