Home Labarai 2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile...

2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile Jam’iyyun Adawa

Biyo bayan rahotannin da ke cewa gwamnatocin jihohin kasar na kokarin dakile ayyukan zaben jam’iyyun adawa da na ‘yan takararsu, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi Allah-wadai da irin wannan dabi’a, inda ta ce a shirye take ta hukunta jihohin da aka samu irin wannan lamari.

A cewar INEC, dukkan jam’iyyun da za su shiga zabukan 2023 suna da ‘yancin gudanar da yakin neman zabe a dukkan jihohin kasar nan 36.

hukumar ta alakatan hakada Jadawalin Ayyuka na yakin neman zaben 2023 na Jam’iyyun siyasa kamar yadda aka tanada a sashe na 94 (1) na dokar zabe ta 2022.

Don haka hukumar ta gargadi gwamnatocin jihohi da kada su hana sauran jam’iyyun siyasa yakin neman zabe a yankunansu.

Babban sakataren yada labarai na shugaban hukumar ta INEC, Mista Rotimi Oyekanmi, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, ya ce akwai hukuncin da ya saba wa wadannan tanade-tanade kuma doka ba zata sassautawa mutum ba komai girman daraja.

Oyekanmi ya ce dokar ta ce za a raba lokacin iska / sararin kafofin watsa labarai na lantarki da na bugu, na jama’a ko na sirri, za a ba su daidai wa daida tsakanin jam’iyyun siyasa ko ‘yan takara a sa’o’i iri ɗaya na ranar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp