Home Labarai 2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile...

2023: INEC ta yi Barazanar Daukar Mataki Kan Jihohin Kasar dake Dakile Jam’iyyun Adawa

Biyo bayan rahotannin da ke cewa gwamnatocin jihohin kasar na kokarin dakile ayyukan zaben jam’iyyun adawa da na ‘yan takararsu, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi Allah-wadai da irin wannan dabi’a, inda ta ce a shirye take ta hukunta jihohin da aka samu irin wannan lamari.

A cewar INEC, dukkan jam’iyyun da za su shiga zabukan 2023 suna da ‘yancin gudanar da yakin neman zabe a dukkan jihohin kasar nan 36.

hukumar ta alakatan hakada Jadawalin Ayyuka na yakin neman zaben 2023 na Jam’iyyun siyasa kamar yadda aka tanada a sashe na 94 (1) na dokar zabe ta 2022.

Don haka hukumar ta gargadi gwamnatocin jihohi da kada su hana sauran jam’iyyun siyasa yakin neman zabe a yankunansu.

Babban sakataren yada labarai na shugaban hukumar ta INEC, Mista Rotimi Oyekanmi, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, ya ce akwai hukuncin da ya saba wa wadannan tanade-tanade kuma doka ba zata sassautawa mutum ba komai girman daraja.

Oyekanmi ya ce dokar ta ce za a raba lokacin iska / sararin kafofin watsa labarai na lantarki da na bugu, na jama’a ko na sirri, za a ba su daidai wa daida tsakanin jam’iyyun siyasa ko ‘yan takara a sa’o’i iri ɗaya na ranar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp