Home Labarai ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

Alamu masu karfi na nuni da cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta kwashe kusan shekara guda ta shiga zai kawo karshe a karshen mako.

Hakan ya biyo bayan kyakkyawan sakamako da aka samu a zaman da kungiyar ta yi da majalisar wakilai karkashin jagorancin Hon Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila da shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, a ganawarsu ta karshe da sun ce “Za a kawo karshen yajin aikin nan da kwanaki” sannan kuma ya ce “akwai gagarumar nasara bayan lokacin da aka dauka ana cikin halin yajin aikin.

Yanzu haka dai majiyoyi daga ASUU sun bayyanawa cewa idan al’amura suka tafi kamar yadda aka tsara a wannan makon, za a yi sanarwar kawo karshen yajin aikin na tsawon watanni 8 ko kuma kafin Juma’a.

Yayin da ake sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bayyana matakin karshe na gwamnati bisa shawarwarin Gbajabiamila a ranar Talata, shugabannin kungiyar ASUU na shiyya-shiyya kuma suna yin taro don duba cancantar shawarwarin da shugaban majalisar ya bayar wanda ake ganin ya tilastawa bangarorin biyu yin dabaru.

A cikin jadawalin ayyukan da majiyoyin suka rabawa manema labarai, kungiyar za ta gudanar da wani taro a  Laraba domin mayar da martani kan jawabin da shugaba Buhari ya yi a ranar Talata.

Majalisar za ta yi la’akari da shawarar da shugaban kasa ya yanke da kuma rangwamen da ya dace don kawo karshen yajin aikin.

A bisa ka’ida, babbar kungiyar ASUU ta yanke shawara, wato kwamitin zartarwa na kasa, NEC, zai yi zama a ranar Alhamis don yanke shawara kan ra’ayoyin da aka tattara daga tarukan farko.

A cewar majiyoyin, idan taron hukumar ya tsawaita har zuwa yammacin ranar Alhamis, za a sanar da matakin karshe a ranar Juma’a.

“Idan abubuwa suka tafi yadda aka tsara, tsakanin Alhamis zuwa Juma’a a janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp