Home Labarai ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

Alamu masu karfi na nuni da cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta kwashe kusan shekara guda ta shiga zai kawo karshe a karshen mako.

Hakan ya biyo bayan kyakkyawan sakamako da aka samu a zaman da kungiyar ta yi da majalisar wakilai karkashin jagorancin Hon Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila da shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, a ganawarsu ta karshe da sun ce “Za a kawo karshen yajin aikin nan da kwanaki” sannan kuma ya ce “akwai gagarumar nasara bayan lokacin da aka dauka ana cikin halin yajin aikin.

Yanzu haka dai majiyoyi daga ASUU sun bayyanawa cewa idan al’amura suka tafi kamar yadda aka tsara a wannan makon, za a yi sanarwar kawo karshen yajin aikin na tsawon watanni 8 ko kuma kafin Juma’a.

Yayin da ake sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bayyana matakin karshe na gwamnati bisa shawarwarin Gbajabiamila a ranar Talata, shugabannin kungiyar ASUU na shiyya-shiyya kuma suna yin taro don duba cancantar shawarwarin da shugaban majalisar ya bayar wanda ake ganin ya tilastawa bangarorin biyu yin dabaru.

A cikin jadawalin ayyukan da majiyoyin suka rabawa manema labarai, kungiyar za ta gudanar da wani taro a  Laraba domin mayar da martani kan jawabin da shugaba Buhari ya yi a ranar Talata.

Majalisar za ta yi la’akari da shawarar da shugaban kasa ya yanke da kuma rangwamen da ya dace don kawo karshen yajin aikin.

A bisa ka’ida, babbar kungiyar ASUU ta yanke shawara, wato kwamitin zartarwa na kasa, NEC, zai yi zama a ranar Alhamis don yanke shawara kan ra’ayoyin da aka tattara daga tarukan farko.

A cewar majiyoyin, idan taron hukumar ya tsawaita har zuwa yammacin ranar Alhamis, za a sanar da matakin karshe a ranar Juma’a.

“Idan abubuwa suka tafi yadda aka tsara, tsakanin Alhamis zuwa Juma’a a janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp