Home Labarai ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

ASUU Na Shirin Janye Yajin Aiki Ranar Juma’a

Alamu masu karfi na nuni da cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta kwashe kusan shekara guda ta shiga zai kawo karshe a karshen mako.

Hakan ya biyo bayan kyakkyawan sakamako da aka samu a zaman da kungiyar ta yi da majalisar wakilai karkashin jagorancin Hon Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila da shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, a ganawarsu ta karshe da sun ce “Za a kawo karshen yajin aikin nan da kwanaki” sannan kuma ya ce “akwai gagarumar nasara bayan lokacin da aka dauka ana cikin halin yajin aikin.

Yanzu haka dai majiyoyi daga ASUU sun bayyanawa cewa idan al’amura suka tafi kamar yadda aka tsara a wannan makon, za a yi sanarwar kawo karshen yajin aikin na tsawon watanni 8 ko kuma kafin Juma’a.

Yayin da ake sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bayyana matakin karshe na gwamnati bisa shawarwarin Gbajabiamila a ranar Talata, shugabannin kungiyar ASUU na shiyya-shiyya kuma suna yin taro don duba cancantar shawarwarin da shugaban majalisar ya bayar wanda ake ganin ya tilastawa bangarorin biyu yin dabaru.

A cikin jadawalin ayyukan da majiyoyin suka rabawa manema labarai, kungiyar za ta gudanar da wani taro a  Laraba domin mayar da martani kan jawabin da shugaba Buhari ya yi a ranar Talata.

Majalisar za ta yi la’akari da shawarar da shugaban kasa ya yanke da kuma rangwamen da ya dace don kawo karshen yajin aikin.

A bisa ka’ida, babbar kungiyar ASUU ta yanke shawara, wato kwamitin zartarwa na kasa, NEC, zai yi zama a ranar Alhamis don yanke shawara kan ra’ayoyin da aka tattara daga tarukan farko.

A cewar majiyoyin, idan taron hukumar ya tsawaita har zuwa yammacin ranar Alhamis, za a sanar da matakin karshe a ranar Juma’a.

“Idan abubuwa suka tafi yadda aka tsara, tsakanin Alhamis zuwa Juma’a a janye yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp