Home DUNIYA Habasha ta Goyin Bayan Janye Takunkumin Hana Sayen Makamai kan Somalia

Habasha ta Goyin Bayan Janye Takunkumin Hana Sayen Makamai kan Somalia

Gwamnatin Somalia na samun goyon baya kan fafutukar da ta ke na ganin an janye takunkumin da aka kakaba mata na hana shigar da makamai kasar, inda a baya bayan nan, Habasha ta bi sahun Uganda wajen goyon bayan janye matakin.

A cikin watan Nuwamba ake sa ran kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri’a kan sabunta takunkumin haramta saidawa Somalia makamai, wanda gwamnati ta ce, cire shi zai taimaka mata wajen yakar mayakan ‘yan ta’adda na Al Shebaab.

Goyon bayan da Habasha ta bai wa Somalia, ya zo ne bayan da a watan Yuli, gungun mayakan Al Shebaab suka kutsa cikin iyakarta, a lokacin da su ke gujewa hare-haren sojojin Somalia.

A halin yanzu, shekaru akalla 30 kenan aka shafe takunkuman hana shigar da makaman na aiki kan Somalia, wadanda shugaban kasar Hassan Sheikh Mohamud da Firaministan Habasha Abiy Ahmed suka ce lokaci ya yi da za a janye su, domin ba da damar kaddamar da cikakken yaki kan mayakan Al Shebaab.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp