Home DUNIYA Habasha ta Goyin Bayan Janye Takunkumin Hana Sayen Makamai kan Somalia

Habasha ta Goyin Bayan Janye Takunkumin Hana Sayen Makamai kan Somalia

Gwamnatin Somalia na samun goyon baya kan fafutukar da ta ke na ganin an janye takunkumin da aka kakaba mata na hana shigar da makamai kasar, inda a baya bayan nan, Habasha ta bi sahun Uganda wajen goyon bayan janye matakin.

A cikin watan Nuwamba ake sa ran kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri’a kan sabunta takunkumin haramta saidawa Somalia makamai, wanda gwamnati ta ce, cire shi zai taimaka mata wajen yakar mayakan ‘yan ta’adda na Al Shebaab.

Goyon bayan da Habasha ta bai wa Somalia, ya zo ne bayan da a watan Yuli, gungun mayakan Al Shebaab suka kutsa cikin iyakarta, a lokacin da su ke gujewa hare-haren sojojin Somalia.

A halin yanzu, shekaru akalla 30 kenan aka shafe takunkuman hana shigar da makaman na aiki kan Somalia, wadanda shugaban kasar Hassan Sheikh Mohamud da Firaministan Habasha Abiy Ahmed suka ce lokaci ya yi da za a janye su, domin ba da damar kaddamar da cikakken yaki kan mayakan Al Shebaab.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp