Home DUNIYA An yi Musayar Fursunoni Tsakanin Rasha da Ukraine

An yi Musayar Fursunoni Tsakanin Rasha da Ukraine

Gwamnatin Ukraine ta sanar da yin musayar fursunoni sama da 100 tsakaninta da Rasha, musayar da ta ce ita ce ta farko da ta kunshi mata zalla, bayan shafe kusan watanni takwas suna gwabza yaki.

Shugaban ma’aikatar fadar shugaban Ukraine Andriy Yermak ya ce mata 108 suka samu nasarar kubutarwa yayin musayar fursunonin da suka yi da Rasha.

Yermak ya ce wasu daga cikin mutanen da aka yi musayar karbarsu daga hannun sojojin Rasha, iyaye ne da ‘yayansu mata da aka tsare su tare, yayin kawanyar da dakarun mamaya suka yi wa kamfanin sarrafa karafa na Azovstal da ke birnin Mariupol.

A cikin jawabinsa na yau da kullun da yammacin ranar Litinin, shugaba Vlodymyr Zelensky ya ce 96 daga cikin fursunonin da aka yi musanya sojoji ne mata, 12 kuma fararen hula.

Ita kuwa ma’aikatar tsaron Rasha ta ce mutanenta 72 da suka dawo daga Ukraine ma’aikatan wani jirgin ruwa ne na fararen hula da Ukraine ta tsare su tun a watan Fabrairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp