Home DUNIYA An yi Musayar Fursunoni Tsakanin Rasha da Ukraine

An yi Musayar Fursunoni Tsakanin Rasha da Ukraine

Gwamnatin Ukraine ta sanar da yin musayar fursunoni sama da 100 tsakaninta da Rasha, musayar da ta ce ita ce ta farko da ta kunshi mata zalla, bayan shafe kusan watanni takwas suna gwabza yaki.

Shugaban ma’aikatar fadar shugaban Ukraine Andriy Yermak ya ce mata 108 suka samu nasarar kubutarwa yayin musayar fursunonin da suka yi da Rasha.

Yermak ya ce wasu daga cikin mutanen da aka yi musayar karbarsu daga hannun sojojin Rasha, iyaye ne da ‘yayansu mata da aka tsare su tare, yayin kawanyar da dakarun mamaya suka yi wa kamfanin sarrafa karafa na Azovstal da ke birnin Mariupol.

A cikin jawabinsa na yau da kullun da yammacin ranar Litinin, shugaba Vlodymyr Zelensky ya ce 96 daga cikin fursunonin da aka yi musanya sojoji ne mata, 12 kuma fararen hula.

Ita kuwa ma’aikatar tsaron Rasha ta ce mutanenta 72 da suka dawo daga Ukraine ma’aikatan wani jirgin ruwa ne na fararen hula da Ukraine ta tsare su tun a watan Fabrairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp