Home DUNIYA Shugaban kasar Afirka ta Kudu yace sun Damuwa da yadda kasashen duniya...

Shugaban kasar Afirka ta Kudu yace sun Damuwa da yadda kasashen duniya suka kauda kansu daga fafutukar samun yancin Yammacin Sahara

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya sake jaddada goyan bayan kasar sa ga Yammacin Sahara don ganin ta zama kasa mai cin gashin kan ta daga kasar Morocco.

Ramaphosa ya bayyana haka ne lokacin da ya karbi shugaban kungiyar Polisario dake fafutukar kafa kasar Yammacin Saharar, Brahim Ghali wanda ya ziyarce shi a Pretoria.

Shugaban kasar yace suna matukar damuwa da yadda kasashen duniya suka kauda kansu daga fafutukar samun yancin Yammacin Sahara wadda kasar Morocco ta yiwa kamun kazar kuku.

Ramaphosa yace su a Afirka ta Kudu sun fahimci muhimmancin wannan fafutuka ta samun yancin kan yankin, kuma suna bayyana goyan bayan su dari-bisa-dari wajen ganin an samu nasarar yancin yankin domin baiwa jama’ar yankin abinda suke bukata.

Shugaban ya danganta fafutukar ‘yancin Yammacin Sahara da na yaki da wariyar jinsin kasarsu ta Afirka ta Kudu tayi, inda ya bayyana su a matsayin halartattun yake yaken da suka zama wajibi.

Kungiyar Polisario na fafutukar samun ‘yanci kai tun daga shekarar 1976, abinda ya sa ta fada rikici da Morocco wadda ta mamaye ta tun bayan mulkin mallakar da Spain ta yiwa yankin tsakanin shekarar 1884 zuwa 1975.

Kungiyar Polisario tace akalla kasashe 80 sun amince da fafutukar su, amma kuma Morocco taki amincewa ta bata ‘yancin kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp