Jonathan ya Rabauta da Lambar Yabo ta Shugaba Na Gari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayar da kyautar lambar girman shugabanci na gari akan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan da wasu fitattaun ‘yan Najeriya 43.

Ita dai wannan lambar girma an ware ta ne ta musamman domin girmama wasu jama’ar kasar da suka bada gudumawa a matakin kasa ko jiha ko kananan hukumomi ko kuma ayyukan gwamnati ko na jinkai.

Sharuddan karbar lambar girma sun hada da bada gudumawa a matsayin ma’aikacin jama’a ko kuma fice a aikin da mutum yake yi na kansa ko nuna rayuwa ta gari a tsakanin jama’a ko yin wani aikin da jama’a zasu ci gajiyar sa.

Ana saran ma’aikaci ya nuna a bayyana yadda yake gudanar da aikin sa fiye da yadda ake bukata a tsakanin al’umma.

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 57 minutes 47 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 39 minutes 12 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com