Home Labarai Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Rundunar sojin Nijeriya ta jaddada kudirinta na hada kai da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro domin samar da cikakken tsaro da kuma tabbatar da an gudanar da zaben shekarar 2023 cikin kwanciyar hankali.

Babban kwamandan rundunar sojojin Najeriya ta 7, Manjo Janar. Waidi Shuaib, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma daya kaiwa kwamishinan ‘yan sanda jihar Borno, Abdu Umar, a birnin Maiduguri ranar Talata.

Ya ce hada kai tsakanin sojoji da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro zai taimaka wajen samar da tsaro mai yawa kafin zabuka da kuma bayan babban zabe.

GOC ya ce ziyarar za ta ba shi damar yi masa fashin tunani game da shirye-shiryen ‘yan sanda don magance matsalolin tsaro a lokacin zabe.

Mista Abdu ya ce rundunar ‘yan sandan za ta ci gaba da hada kai da sojoji domin kare rayuka da dukiyoyi a Borno, kuma rundunar ta zafafa sintiri tare da hadin gwiwar rundunonin sojoji domin yakar munanan laifuka a cikin birnin Maiduguri.

Shugaban ‘yan sandan ya sake nanata shirin ‘yan sandan na samar da tsaro domin gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci da kwanciyar hankali.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp