Home General EFCC ta yabawa CBN bisa Matakin Sauya Fasalin Wasu Takardun Kudin Nijeriya.

EFCC ta yabawa CBN bisa Matakin Sauya Fasalin Wasu Takardun Kudin Nijeriya.

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta yabawa babban banki na kasa bisa matakin sake fasalin wasu  takardun kudin kasar.

Yabon na kunshe ne cikin wata sanarwa da  mai Magana da yawun hukumar Wilson Uwajaren ya fitar bayan taron manema labarai a ranar Laraba a birnin Abuja.

Da yake bayani kan matakin, shugaban hukumar EFCC AbdulRasheed Bawa, yace  matakin ya zo daidai lokacin da ake bukata, mussaman duba da kalubalen da  ake fuskanta ta bangaren kudi, wanda yace ya haifar da koma baya  ga tsare-tsaren hada-hadar kudade

Haka kuma ya bukaci bngaren hada-hadar kudi da cibiyoyin musayar kudaden ketare da su yi aiki bisa sharuddan da  babban bankin ya gindaya, na ganin an janye tsaffin takardar kudi, yana mai gargadin cewa hukumar ta EFCC za ta sa ido na ganin baragurbi basu kawo cikas ga ci gaban ba.

Tare da kira ga bankuna da su yi watsi da duk wani  kokari da za a yi amfani da sun a ganin ba a cimma nasara ga Shirin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp