Home General EFCC ta yabawa CBN bisa Matakin Sauya Fasalin Wasu Takardun Kudin Nijeriya.

EFCC ta yabawa CBN bisa Matakin Sauya Fasalin Wasu Takardun Kudin Nijeriya.

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta yabawa babban banki na kasa bisa matakin sake fasalin wasu  takardun kudin kasar.

Yabon na kunshe ne cikin wata sanarwa da  mai Magana da yawun hukumar Wilson Uwajaren ya fitar bayan taron manema labarai a ranar Laraba a birnin Abuja.

Da yake bayani kan matakin, shugaban hukumar EFCC AbdulRasheed Bawa, yace  matakin ya zo daidai lokacin da ake bukata, mussaman duba da kalubalen da  ake fuskanta ta bangaren kudi, wanda yace ya haifar da koma baya  ga tsare-tsaren hada-hadar kudade

Haka kuma ya bukaci bngaren hada-hadar kudi da cibiyoyin musayar kudaden ketare da su yi aiki bisa sharuddan da  babban bankin ya gindaya, na ganin an janye tsaffin takardar kudi, yana mai gargadin cewa hukumar ta EFCC za ta sa ido na ganin baragurbi basu kawo cikas ga ci gaban ba.

Tare da kira ga bankuna da su yi watsi da duk wani  kokari da za a yi amfani da sun a ganin ba a cimma nasara ga Shirin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp