Home DUNIYA Jami’an Tsaron Sun Bude Wuta kan Masu Zanga-Zanga a Iran

Jami’an Tsaron Sun Bude Wuta kan Masu Zanga-Zanga a Iran

Rahotannin daga kasar Iran na bayyana cewa Jami’an tsaro sun bude wuta kan dandazon masu zanga-zangar cika kwanaki 40 da kisan matashiya Mahsa Amini inda mutane da dama suka jikkata, ciki har da wadanda suka yi dafifi a kabarin matashiyar.

Dubunnan masu zanga-zangar kisan Mahsa Amini sun yi dafifi a kabarin matashiyar da ke yankin Saqez don jimamin cika kwanaki 40 da kisan da aka yi mata, duk kuwa da matakan tsaron da gwamnatin kasar ta sanya don hana gangamin a yau laraba.

Baya ga wadanda suka yi dafifi a makabarta da aka birne Mahsa wasu dubunnan masu zanga-zangar na daban sun taru a dandalin Zindan da ke cikin garin na Saqez a yammacin yankin Kurdawa lamarin da ya sanya jami’an tsaro bude wuta tare da amfani da hayaki mai sanya hawaye don tarwatsa dandazon.

Wani faifan bidiyo da tuni ya fara yawo a kafafen sada zumunta sun nuna yadda jami’an ‘yan sandan ke amfani da karfin wajen tarwatsa masu zanga-zangar, wanda wata kungiyar kare hakkin dan adam ta kasar Norway da ke sanya idanu a zanga-zangar ta Iran ke cewa matakin da jami’an suka dauka ya take dokokin hakkin masu gangamin.

Dubun-dubatar ‘yan kasar ta Iran galibi mata ne ke ci gaba da zanga-zanga don nuna bacin ransu game da kisan matsahiya Amini mai shekaru 22 kwanaki 3 bayan jami’an tabbatar da da a sun kame ta bisa laifin kin saka hijabi.

Fiye da wata guda ana ci gaba da zanga-zangar a sassan Iran wadda ta samu goyon baya daga kasashe daban-daban yayinda ta janyowa kasar karin takunkumai daga ketare, sai dai gangamin ya sake karfafa a yau ne dai dai lokacin da ake kammala makokin kwanaki 40 da bisa al’ada ake yiwa kowanne mamaci a Iran.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp