Home DUNIYA Jami’an Tsaron Sun Bude Wuta kan Masu Zanga-Zanga a Iran

Jami’an Tsaron Sun Bude Wuta kan Masu Zanga-Zanga a Iran

Rahotannin daga kasar Iran na bayyana cewa Jami’an tsaro sun bude wuta kan dandazon masu zanga-zangar cika kwanaki 40 da kisan matashiya Mahsa Amini inda mutane da dama suka jikkata, ciki har da wadanda suka yi dafifi a kabarin matashiyar.

Dubunnan masu zanga-zangar kisan Mahsa Amini sun yi dafifi a kabarin matashiyar da ke yankin Saqez don jimamin cika kwanaki 40 da kisan da aka yi mata, duk kuwa da matakan tsaron da gwamnatin kasar ta sanya don hana gangamin a yau laraba.

Baya ga wadanda suka yi dafifi a makabarta da aka birne Mahsa wasu dubunnan masu zanga-zangar na daban sun taru a dandalin Zindan da ke cikin garin na Saqez a yammacin yankin Kurdawa lamarin da ya sanya jami’an tsaro bude wuta tare da amfani da hayaki mai sanya hawaye don tarwatsa dandazon.

Wani faifan bidiyo da tuni ya fara yawo a kafafen sada zumunta sun nuna yadda jami’an ‘yan sandan ke amfani da karfin wajen tarwatsa masu zanga-zangar, wanda wata kungiyar kare hakkin dan adam ta kasar Norway da ke sanya idanu a zanga-zangar ta Iran ke cewa matakin da jami’an suka dauka ya take dokokin hakkin masu gangamin.

Dubun-dubatar ‘yan kasar ta Iran galibi mata ne ke ci gaba da zanga-zanga don nuna bacin ransu game da kisan matsahiya Amini mai shekaru 22 kwanaki 3 bayan jami’an tabbatar da da a sun kame ta bisa laifin kin saka hijabi.

Fiye da wata guda ana ci gaba da zanga-zangar a sassan Iran wadda ta samu goyon baya daga kasashe daban-daban yayinda ta janyowa kasar karin takunkumai daga ketare, sai dai gangamin ya sake karfafa a yau ne dai dai lokacin da ake kammala makokin kwanaki 40 da bisa al’ada ake yiwa kowanne mamaci a Iran.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp