Home DUNIYA Jami’an Tsaron Sun Bude Wuta kan Masu Zanga-Zanga a Iran

Jami’an Tsaron Sun Bude Wuta kan Masu Zanga-Zanga a Iran

Rahotannin daga kasar Iran na bayyana cewa Jami’an tsaro sun bude wuta kan dandazon masu zanga-zangar cika kwanaki 40 da kisan matashiya Mahsa Amini inda mutane da dama suka jikkata, ciki har da wadanda suka yi dafifi a kabarin matashiyar.

Dubunnan masu zanga-zangar kisan Mahsa Amini sun yi dafifi a kabarin matashiyar da ke yankin Saqez don jimamin cika kwanaki 40 da kisan da aka yi mata, duk kuwa da matakan tsaron da gwamnatin kasar ta sanya don hana gangamin a yau laraba.

Baya ga wadanda suka yi dafifi a makabarta da aka birne Mahsa wasu dubunnan masu zanga-zangar na daban sun taru a dandalin Zindan da ke cikin garin na Saqez a yammacin yankin Kurdawa lamarin da ya sanya jami’an tsaro bude wuta tare da amfani da hayaki mai sanya hawaye don tarwatsa dandazon.

Wani faifan bidiyo da tuni ya fara yawo a kafafen sada zumunta sun nuna yadda jami’an ‘yan sandan ke amfani da karfin wajen tarwatsa masu zanga-zangar, wanda wata kungiyar kare hakkin dan adam ta kasar Norway da ke sanya idanu a zanga-zangar ta Iran ke cewa matakin da jami’an suka dauka ya take dokokin hakkin masu gangamin.

Dubun-dubatar ‘yan kasar ta Iran galibi mata ne ke ci gaba da zanga-zanga don nuna bacin ransu game da kisan matsahiya Amini mai shekaru 22 kwanaki 3 bayan jami’an tabbatar da da a sun kame ta bisa laifin kin saka hijabi.

Fiye da wata guda ana ci gaba da zanga-zangar a sassan Iran wadda ta samu goyon baya daga kasashe daban-daban yayinda ta janyowa kasar karin takunkumai daga ketare, sai dai gangamin ya sake karfafa a yau ne dai dai lokacin da ake kammala makokin kwanaki 40 da bisa al’ada ake yiwa kowanne mamaci a Iran.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp