Home DUNIYA Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Watanni biyu bayan samun nasarar lashe zaben shugaban kasar Kenya William Ruto ya rantsar da kunshin majalisar ministocin a ranar Alhamis.

Ministocin guda 12 an rantsar dasu ne domin tunkarar matsalolin da suka addabi kasar da suka hada da tsadar rayuwa da kuma sauran batutuwa suka shafi tattalin Arziki a kasar dake gabashin nahiyar Afirka, wanda wannan na cikin alkawurran da Ruto ya dauka yayin yakin neman zaben sa.

Sai dai kuma ana kallon sabuwar majalisar da Ruto ya kafa bata cimma daidaiton jinsi ba kamar yadda ya alkawurta tun a yakin neman zaben nasa, inda aka bayyana sunayen mata 7 kawai.

Tsohon mataimakain shugaban kasar kuma tsohon dan adawar Raila Odinga daya marawa Ruto baya Musalia Mudavadi ya zama sabon sakataren firaministan kasar da aka kirkiro.

Sai kuma Alfred tsohon gwamna wanda jam’iyyar sa ta goyi bayan Ruto shi ne zai jagoranci ma’aikatar harkokin wajen kasar.

Kithure Kindiki, wand ana cikin lauyoyin da suka kare zaben Ruto a watan Agusta, shine zai jagoranci ma’aikatar cikin gida mai karfi.

Kindiki shine wanda ya wakilci Ruto a shari’ar da ake yi masa a Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa dake birnin Hague lokacin da aka zrge shi da hannu wajen kitsa tarzomar da ta biyo bayan zaben 2007- 2008 wanda yayi sanadin mutuwar mutane akall 1,100 tare da raba sama da 600,000 da muhallansu.

Sai kuma ma’ajin kasar da Njuguna Ndung’u zai jagoranta, wanda shine tsohon gwamnan babban bankin kasar.

 PRNigeria Hausa

(AFRICA NEWS)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp