Home DUNIYA Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Watanni biyu bayan samun nasarar lashe zaben shugaban kasar Kenya William Ruto ya rantsar da kunshin majalisar ministocin a ranar Alhamis.

Ministocin guda 12 an rantsar dasu ne domin tunkarar matsalolin da suka addabi kasar da suka hada da tsadar rayuwa da kuma sauran batutuwa suka shafi tattalin Arziki a kasar dake gabashin nahiyar Afirka, wanda wannan na cikin alkawurran da Ruto ya dauka yayin yakin neman zaben sa.

Sai dai kuma ana kallon sabuwar majalisar da Ruto ya kafa bata cimma daidaiton jinsi ba kamar yadda ya alkawurta tun a yakin neman zaben nasa, inda aka bayyana sunayen mata 7 kawai.

Tsohon mataimakain shugaban kasar kuma tsohon dan adawar Raila Odinga daya marawa Ruto baya Musalia Mudavadi ya zama sabon sakataren firaministan kasar da aka kirkiro.

Sai kuma Alfred tsohon gwamna wanda jam’iyyar sa ta goyi bayan Ruto shi ne zai jagoranci ma’aikatar harkokin wajen kasar.

Kithure Kindiki, wand ana cikin lauyoyin da suka kare zaben Ruto a watan Agusta, shine zai jagoranci ma’aikatar cikin gida mai karfi.

Kindiki shine wanda ya wakilci Ruto a shari’ar da ake yi masa a Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa dake birnin Hague lokacin da aka zrge shi da hannu wajen kitsa tarzomar da ta biyo bayan zaben 2007- 2008 wanda yayi sanadin mutuwar mutane akall 1,100 tare da raba sama da 600,000 da muhallansu.

Sai kuma ma’ajin kasar da Njuguna Ndung’u zai jagoranta, wanda shine tsohon gwamnan babban bankin kasar.

 PRNigeria Hausa

(AFRICA NEWS)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp