Home DUNIYA Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Kenya: Ruto ya Rantsar da Kunshen Majalisar Ministocin

Watanni biyu bayan samun nasarar lashe zaben shugaban kasar Kenya William Ruto ya rantsar da kunshin majalisar ministocin a ranar Alhamis.

Ministocin guda 12 an rantsar dasu ne domin tunkarar matsalolin da suka addabi kasar da suka hada da tsadar rayuwa da kuma sauran batutuwa suka shafi tattalin Arziki a kasar dake gabashin nahiyar Afirka, wanda wannan na cikin alkawurran da Ruto ya dauka yayin yakin neman zaben sa.

Sai dai kuma ana kallon sabuwar majalisar da Ruto ya kafa bata cimma daidaiton jinsi ba kamar yadda ya alkawurta tun a yakin neman zaben nasa, inda aka bayyana sunayen mata 7 kawai.

Tsohon mataimakain shugaban kasar kuma tsohon dan adawar Raila Odinga daya marawa Ruto baya Musalia Mudavadi ya zama sabon sakataren firaministan kasar da aka kirkiro.

Sai kuma Alfred tsohon gwamna wanda jam’iyyar sa ta goyi bayan Ruto shi ne zai jagoranci ma’aikatar harkokin wajen kasar.

Kithure Kindiki, wand ana cikin lauyoyin da suka kare zaben Ruto a watan Agusta, shine zai jagoranci ma’aikatar cikin gida mai karfi.

Kindiki shine wanda ya wakilci Ruto a shari’ar da ake yi masa a Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa dake birnin Hague lokacin da aka zrge shi da hannu wajen kitsa tarzomar da ta biyo bayan zaben 2007- 2008 wanda yayi sanadin mutuwar mutane akall 1,100 tare da raba sama da 600,000 da muhallansu.

Sai kuma ma’ajin kasar da Njuguna Ndung’u zai jagoranta, wanda shine tsohon gwamnan babban bankin kasar.

 PRNigeria Hausa

(AFRICA NEWS)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp