Home Labarai Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Rundunar sojin Nijeriya ta jaddada kudirinta na hada kai da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro domin samar da cikakken tsaro da kuma tabbatar da an gudanar da zaben shekarar 2023 cikin kwanciyar hankali.

Babban kwamandan rundunar sojojin Najeriya ta 7, Manjo Janar. Waidi Shuaib, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma daya kaiwa kwamishinan ‘yan sanda jihar Borno, Abdu Umar, a birnin Maiduguri ranar Talata.

Ya ce hada kai tsakanin sojoji da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro zai taimaka wajen samar da tsaro mai yawa kafin zabuka da kuma bayan babban zabe.

GOC ya ce ziyarar za ta ba shi damar yi masa fashin tunani game da shirye-shiryen ‘yan sanda don magance matsalolin tsaro a lokacin zabe.

Mista Abdu ya ce rundunar ‘yan sandan za ta ci gaba da hada kai da sojoji domin kare rayuka da dukiyoyi a Borno, kuma rundunar ta zafafa sintiri tare da hadin gwiwar rundunonin sojoji domin yakar munanan laifuka a cikin birnin Maiduguri.

Shugaban ‘yan sandan ya sake nanata shirin ‘yan sandan na samar da tsaro domin gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci da kwanciyar hankali.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp