Home Labarai Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Rundunar sojin Nijeriya ta jaddada kudirinta na hada kai da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro domin samar da cikakken tsaro da kuma tabbatar da an gudanar da zaben shekarar 2023 cikin kwanciyar hankali.

Babban kwamandan rundunar sojojin Najeriya ta 7, Manjo Janar. Waidi Shuaib, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma daya kaiwa kwamishinan ‘yan sanda jihar Borno, Abdu Umar, a birnin Maiduguri ranar Talata.

Ya ce hada kai tsakanin sojoji da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro zai taimaka wajen samar da tsaro mai yawa kafin zabuka da kuma bayan babban zabe.

GOC ya ce ziyarar za ta ba shi damar yi masa fashin tunani game da shirye-shiryen ‘yan sanda don magance matsalolin tsaro a lokacin zabe.

Mista Abdu ya ce rundunar ‘yan sandan za ta ci gaba da hada kai da sojoji domin kare rayuka da dukiyoyi a Borno, kuma rundunar ta zafafa sintiri tare da hadin gwiwar rundunonin sojoji domin yakar munanan laifuka a cikin birnin Maiduguri.

Shugaban ‘yan sandan ya sake nanata shirin ‘yan sandan na samar da tsaro domin gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci da kwanciyar hankali.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp