Home Labarai Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Zaben 2023: Jami’an Tsaron Nijeriya Sun yi Alkawarin Samar da Tsaro

Rundunar sojin Nijeriya ta jaddada kudirinta na hada kai da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro domin samar da cikakken tsaro da kuma tabbatar da an gudanar da zaben shekarar 2023 cikin kwanciyar hankali.

Babban kwamandan rundunar sojojin Najeriya ta 7, Manjo Janar. Waidi Shuaib, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma daya kaiwa kwamishinan ‘yan sanda jihar Borno, Abdu Umar, a birnin Maiduguri ranar Talata.

Ya ce hada kai tsakanin sojoji da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro zai taimaka wajen samar da tsaro mai yawa kafin zabuka da kuma bayan babban zabe.

GOC ya ce ziyarar za ta ba shi damar yi masa fashin tunani game da shirye-shiryen ‘yan sanda don magance matsalolin tsaro a lokacin zabe.

Mista Abdu ya ce rundunar ‘yan sandan za ta ci gaba da hada kai da sojoji domin kare rayuka da dukiyoyi a Borno, kuma rundunar ta zafafa sintiri tare da hadin gwiwar rundunonin sojoji domin yakar munanan laifuka a cikin birnin Maiduguri.

Shugaban ‘yan sandan ya sake nanata shirin ‘yan sandan na samar da tsaro domin gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci da kwanciyar hankali.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp