Home Labarai Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin...

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar, nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin nasa.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

https://timesng.com/naira-black-market-exchange-rate-today/

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya Nijeriya tayi watsi da shirin CBN na sauya fasalin kudin Kasar.

Bayan Sa’oi 48 da Gwamnan babban bankin Nijeriya CBN, Godwin Emefiele ya sanar da kudirin sa na sauya fasalin kudin kasar nan da 15 ga watan Disambar 2022, Gwamnatin tarayyar kasar ta barranta kanta da yunkurin.

Ministar kudi kasafi da tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan, inda tace sauya fasalin kudin ka iya haifar da gagarumin tasgaro ga Kasar dama tattalin arzikin kasar.

yayin da take amsa tambayoyi a wurin kare kasafin kudin ma’akatar ta  gaban majalisar bayan da sanata Opeyemi Bamidele ya tambaye ta inda ta gargadi CBN kan abinda kaje kazo kan lamarin sauya fasalin kudin.

Sanata Bamidele yayi tambayan ko mene yasa kwanaki biyu bayan bayyana kudin sauya fasalin kudin dalar Amurka ta tashi daga 740 zuwa 788 sakamakon rige-rigen da ake na sauya kudin zuwa dalar Amurka.

Idan za’a iya tunawa a ranar Laraba Gwamnan Babban Bankin na CBN  Emefiele bankin zai sauya fasalin takardun kudin kasar daga naira 200 har zuwa 1000.

Emefiele yace an dauki wannan mataki ne kasancewar yadda ake tasarrufi da kudaden kuma CBN bazai bari ake mu’amala da kudin taci-barkatai ba.

Yace sun dogara ne da sashe na 19 karamin kashi na A da B na dokar babban bankin ta shekarar 2007, wadda ta baiwa hukumar bankin dama bisa sahalewar shugaba Muhammadu Buhari su sauya fasalin kudin kasar daga kan 200 zuwa 1000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp